Thursday, 14 February 2013

Iyalan masu rigakafin polio da aka kashe sun samu tallafi

 Wata jami'ar rigakafin  shan inna

Iyalan ma'aikatan rigakafin shan inna ko polio da aka kashe a jihar Kano a makon jiya, sun samu tallafin naira miliyan daya kowannensu.
Gwamnatin jihar ce ta basu naira dubu dari biyar, yayin da shahararren mai kudin nan na Najeriya, kuma dan asalin jihar Aliko Dangote, kuma ya basu tallafin naira dubu 500.
Kimanin mata tara ne suka mutu a lokacin da wasu 'yan bidiga suka bude musu wuta a ranar Juma'ar data gabata.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake sa ran ministan lafiya na kasar zai kai ziyara jihar Kano game da harin.

No comments:

Post a Comment