Thursday, 21 February 2013

Akalla mutane 8 sun halaka a Maiduguri

 MD Abubakar, babban Spetan 'yan sandan Najeriya

Rahotanni daga Maiduguri, babban birnin jihar Borno na cewa, akalla mutane takwas ne su ka mutu sanadiyar fashewar wani abu da ake kyautata zaton bam ne a unguwar kwastan.
Bakin hayaki ya turnike sararin samania kamar yadda shaidun gani da iddo su ka tabbatar, tare da cewa Shaguna da dama da su ka kone.
Wasu magidanta a Maidugurin sun tabbatar wa da cewa sun ga gawawwakin mutane a kwance.
Wannan al'amari dai ya kara janyo zaman zulumi a birnin.
Ko a ranar laraba ma dai, wasu mutane uku sun mutu bayan fashewar wani abu a birnin Maidugurin.

No comments:

Post a Comment