Thursday, 28 February 2013

'Ya'yan Pele sun bar wasan kwallo

 Andre da Jordan Ayew

Andre da Jordan Ayew sun dakatar da buga wasan kwallo na kasa da kasa, bayan dan rashin jituwa da hukumar kwallon Ghana.
'Yan gida dayan, mai shekaru 23 da kuma 21 na buga wa kulob din Marseille ta Faransa wasa ne.
Kuma sun ce sun dakatar da yin tamaular ne, saboda rikicin dake tsakaninsu da hukumar kwallon Ghana na kara zafi.
An dai cire Andre daga tawagar kwallon kafa ta kasar, da suka je gasar cin kofin zakarun nahiyar Afrika a kasar Afirka ta Kudu, saboda rashin zuwa horo a kan lokaci.
Yayin da kwata-kwata ma ba a sanya dan uwansa Jordan a cikin tawagar ba.
Kuma dukkaninsu sun yarda da cewa maganar tawagar Ghanan ne ya sa suka dakatar da buga kwallo.
'Yan wasan biyu dai 'ya'ya ne ga Abedi Pele Ayew, wanda aka fi sani da Dede, kuma Jordan ne ya rubuta wasiku biyu, da ya aika wa hukumar yana sanar da ita murabus dinsu.
Andre ya ce matsalar da ya samu da masu gudanar da hukumar, ta sa ba zai iya cigaba da buga wasan kwallo ba.
Yayin da shi kuma Jordan yace zai ci gaba da buga kwallo a kulob dinsa, domin ya samu kwarewar da ake bukata wajen sanya shi cikin tawagar kwallon kasar.

Manajan Chelsea zai bar kulob din


                                      Manajan wucin gadi na kulob din Chelsea, Rafael Benitez
                                      Rafael Benitez ya zargi kulob din da bashi mukamin wucin 
                                     gadi, saboda idan bai yi nasara ba su kore shi
Manajan wucingadi na kulob din Chelsea, Rafael Benitez ya ce zai bar kulob din a watan Mayu mai zuwa.
Inda ya bayyana bashi mukamin wucin gadi da kulob din yayi, a matsayin babban kuskure ne.

Benitez ya soki wasu daga cikin masoya kulob din, bayan Middlesbrough ta doke Chelsea da ci biyu da nema, a zagaye na biyar na gasar cin kofin FA.
Ya shaida wa BBC cewa " Chelsea ta bani mukamin manaja na wucin gadi, wanda hakan babban kuskure ne, domin ni manaja ne. "
Ya kara da cewa " Su ma masoya kulob din na taimakawa wajen dagula al'amura. Domin haka kada su damu zan tafi a karshen kakar wasanni."
Hirar da Benitez, wanda tsohon manajan Liverpool ne, ta zo ne bayan wasu magoya bayan kulob din sun nuna adawarsu a gare shi.
Benitez mai shekaru 52 ya yi bakin jini a wajen wasu masoya kulob din, tun bayan da ya karbi jan ragamar kulob din, daga hannun Roberto Di Matteo a watan Nuwamba.

Za a takaita garabasar bankuna a Turai

 Bankin Kungiyar Tarayyar Turai

Masu bankuna a kungiyar Gamayyar Turai za su samu kansu cikin shirin takaita garabasar da ake bai wa masu hannun jari daga shekara mai zuwa.
Wannan ya biyo bayan sakamakon yarjejeniyar da aka cimma a birnin Brussels.

Yarjejeniyar wadda 'yan majalisar kungiyar kasashen Turai ta EU, da wakilan gwamnatoci da jami'ai suka cimma, na daga matakan da aka tsara aiwatar wa domin kare sake aukuwar matsalar durkushewar bankuna.
A karkashin wannan shiri dai za a tsara yawan garabasar da za a bayar ne dai dai da kimar albashin shekara.
Sai dai za a iya kara yawansa amma za a iya yin hakan ne da izinin masu hannun jari kawai.
Bayar da garabasa mai yawan gaske dai ita ake ganin ta haifar da galibin matakan da suka haifar da matsalar tattalin arziki ta 2008,ta kuma kasance tamkar guba ga harkokin siyasa ta yadda ya kai ga tilasta amfani da kudaden gwamnati domin biyan basukan bankunan da suka durkushe.
Wannan mataki dai, wanda wajibi ne mafi yawan kasashen Kungiyar Gamayyar Turai su amince da shi, ana ganin wata galaba ce a kan Birtaniya wadda ita ce babbar matattarar cibiyoyin harkokin kudade a Turai.
Domin tuni daman masu bankuna a birnin Landan suka nuna korafinsu da fargaba a kan tsarin, inda suka ce matakin zai sa a karkatar da harkokin kasuwanci zuwa kasashen da suke wajen kungiyar Gamayyar Turai.

Thailand da Kungiyar Musulmi sun amince da wata yarjejeniya

Kasar Thailand

Gwamnatin Thailand da kungiyar musulmi masu gwagwarmaya sun amince da wata yarjejeniya tattaunawa domin kawo karshen rikicin a kudancin kasar.
Tun shekaru tara suka shude ne 'yan gwagwarmayar suka fara tada kayar baya, lamarin da ya kai ga sanadiyyar rasa rayukan mutane sama da dubu biyar.
Wannan shi ne karon farko da hukumomin Thailand din suka amince da 'yan tawayen,kuma Firaministocin Thailand da Malaysia suka fito fili suka amince da yarjejeniyar.
Dukkannin Kokarin da akayi na kawo karshen fadan ya ci tura.
Wakilin BBC a kudu maso gabashin Asiya ya ce wadanda suke wakiltar 'yan tawayen a wajen tattaunawar daga bangaren dattawan kungiyar, su ne wadanda ke zaune a Malaysia,kuma ba a san wanne irin tasiri suke da shi ba akan galibin matasan kungiyar da suke yaki a Thailand.

Wednesday, 27 February 2013

PDP TA'YI NA'AM DA ZARGINDA GEN BUHARI YAYI MATA.

 

Alhaji Bamanga tukur Shugaban jam'iyyar PDP, Na kasa da sabon shugaban kungiyar gwamnonin PDP zalla, Mr Godswill Akpabio sun furta kalamun da suka gasgata zargin da Janar Muhammadu Buhari ya yi a ranar Litinina Abuja yayin da yake ganawa dazababbun wakilan jam'iyyarsa ta CPC,

inda ya ce jam'iyyar PDP a halin yanzu ta kideme, ta kuma dukufa don ganin ta ci zabe mai zuwa ko ta halin kaka. Alhaji Bamanga ya ce yanzu Shugaba Goodluck Jonathan zai iya shara barci har da
minshari tun da an cire masa kaya, wato an raba shi da shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya, Mr Rotimi Amaechi don ya ki amincewa Jonathan ya yi wasan kura da gwamnoni don daurewa karya gindi wajen tsayar da shi takara a la dole.

Ya furta haka ne sa'ilin da yake marhabin da shugaban sabuwar kungiyar gwamnonin PDP zalla, Mr
Godswil Akpabio sa'ilin da ya kai masa ziyarar ban girma a ofishnsa. Shi ma Mr
Akpbio ya ce jam 'iyyar PDP ta yi shirin tankade duk wadanda ke adawa da sake takarar Shugaba Jonathan, kuma komai girman mukamansu za a yi watsi da su don kar su kawo cikas. E, lalle! Janar Buhari ya yi gaskiya! Jam'iyyar PDP ta kauce daga bisa turbar dimokuradiyya, ta hau ta kama-karya don aiwatar da harkokinta na cikin gida. Abin cewa shi ne a yi dai mu gani, gaba mu bayar da labri wasa ya yi kyau, ko ya kazance! Shure-shure dai bai hana mutuwa.

Sarkin Kano ya koma gida daga london

 Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero
Rahotannin daga Kano a arewacin Nigeria na cewa Mai martaba Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero ya koma gida bayan jinyar da ya yi a London.
Sarkin dai ya yi jinyar ne bayan harin da aka kaiwa ayarin motocin sa ranar 19 ga watan janairu, inda aka kashe wasu daga cikin 'yan tawaggar sa.
Tun bayan hari ne dai, gwamnatin Kanon ta haramta goyan biyu akan babur domin inganta tsaron jahar.
Dubban jama'a ne dai su ka yi dafifi a kofar fadar sarkin su na murnar dawowar sa.

Birtaniya ta gargadi 'yan kasarta a Najeriya

Ministan harkokin wajen Birtaniya

Gwamnatin Birtaniya ta gargadi 'yan kasarta dake zaune a Najeriya, da su guji zuwa wasu jihohi a arewacin Najeriya, biyo bayan karuwar hare-hare da sace mutane a yankin.
Shawarar hana tafiye-tafiyen, wadda aka wallafa a shafin intanet na ofishin jakadancin Birtaniya a Najeriya, ya ce a yanzu yankunan da take shawartar 'yan kasarta su kauce wa kwata-kwata, sun hada da jihar Bauchi da garin Okene na jihar Kogi.
Sauran jihohin da biranen sun hada da Borno da Yobe, da Delta da Bayelsa, da Rivers da kuma Akwa Ibom.
Haka kuma sanarwar ta gardadi 'yan Birtaniya da kada su je biranen, Kano da kuma Warri.
Yayin da kuma Birtaniyar ta ce idan ba tafiyar da ta zama dole ba, kada 'yan kasar su je duk wani yanki dake jihar Kaduna da Kano da Jigawa da Katsina da Gombe da kuma biranen Jos da Riyom da kuma Barikin Ladi a jihar Plato.
Sace-sacen 'yan kasashen waje dai ya karu a arewacin kasar a baya-bayan nan, inda a jihar Bauchi aka sace wasu turawa ma'aikatan kamfanin gine-gine na Setraco ciki har da dan Birtaniya.
Yayin da kawo yanzu babu labarin wani Bafaranshe da aka sace a jihar Katsina, sannan ga Faransawa bakwai da kungiyar nan ta Jama'atu Ahlul Sunna lil da'awati wal jihad ko Boko Haram ta kame a kasar Kamaru kuma take garkuwa da su.
Haka kuma a kudancin kasar, yankin da sace mutane da yin garkuwa da su, ba sabon abu bane, rahotanni sun ce an saki wasu 'yan kasar waje bakwai ma'aikatan jirgin ruwan da aka yi garkuwa da su a jihar Bayelsa.

Tana dabo tsakanin Keshi da NFF

 Mai horar da 'yan wasan Najeriya, Stephen Keshi

Mai horar da 'yan wasan kwallon kafa na Najeriya, Stephen Keshi ya ce rashin jituwar dake tsakaninsa da hukumar kwallon kafa ta kasar, tana kasa tana dabo.
Keshi da ya yi tayin yin murabus, 'yan sa'oi kadan bayan kungiyar Super Eagles ta dauki kofin gasar zakarun kwallon kafa na Afirka, wanda rabon kasar da daukar kofin tun shekarar 1994.

Sai dai ya sauya shawara bayan wani taron gaggawa da ministan wasannin kasar, Bolaji Abdullahi a Johannesburg.
A wani shirin talabijin na turanci, Superspost a ranar Litinin da daddare, Keshi ya ce 'yar masalahar da aka samu tsakaninsu, wacce ta dan so ta kawo tsaiko ga shagulgulan murnar daukar kofin, na wani dan lokaci ne.
"A halin yanzu ina da kyakkyawar dangantaka da shugabana (Aminu Maigari) baya ga mutum daya ko biyu a hukumar" Keshi ya fadi hakan a shirin da ake watsa wa kai tsaye.
Ya kuma kara da cewa "Idan na gaji da zaman da na ke yi, kuma idan har bana jin dadin abin da nake yi, kawai tafiya ta zanyi."
"Sama da kasa ba za ta hade min ba, idan na daina horar da 'yan wasan Najeriya."
"Amma dole a bani girma na, kuma a barni in yi aiki na ba tare da tsoma baki ba." Inji Keshi.
Keshi shi ne bakar fata na biyu da ya taba daukar kofin gasar, a lokacin yana dan wasa da kuma a matsayin mai horar da 'yan wasa a nahiyar Afrika.
Kuma shi ne koci bakar fata na farko, da ya taba daukar kofin tun bayan shekarar 1992.

Radadin satar 'yan kasashen waje a Najeriya

Rundunar 'yan sanda Najeriya ta ce tana ci gaba da bincike

Jama’ar yankin Jama’are dake jihar Bauchi a Najeriya sun bayyana cewa suna jin radadi matuka a harkokin rayuwarsu na yau da kullum da kuma tattalin arziki sakamakon awon gaba da wadansu ma’aikata ’yan kasashen waje na kamfani mafi girma a yankin wato SETRACO.
Kimanin makwanni biyu ke nan dai tun bayan da ’yan bindiga suka sace mutanen bakwai daga gidan kwanan ma’aikata na kamfanin mai aikin gine-gine—musamman na hanyoyin mota—a Najeriya, kuma kawo yanzu babu duriyarsu.
Bayan fruwar lamarin ne dai hukumomin kamfanin suka rufe ayyukansu a yankin na Jama’are sannan suka kwashe ma’aikatansu daga yankin saboda tsaron lafiyarsu.
Sai dai kuma tasirin hakan ta fuskar tattalin arziki shi ne harkoki sun durkushe, daruruwan ’yan Najeriya sun rasa ayyukan yi.

Tsaka mai wuya

Shugaban Majalisar Matasan Jama’are, Malam Hassan Usman, ya shaida BBC cewa al’ummar yankin sun shiga tsaka mai wuya.
“Wannan al’amari ya daga mana hankali, ya ja mana ci baya fiye da kima…matasanmu fiye da dari hudu suna aiki a wannan kamfani; akwai kuma mutane kimanin dari uku ’yan wasu jihohi daban-daban [wadanda] zamansu ya kawo ci gaba tattalin arziki gare mu saboda za su kama haya, za su yi sayayya—kusan rabin albashinsu a wajenmu suke kashe shi.
“Amma sakamakon rufe wannan kamfani zaman banza zai karu, talauci zai karu, da kuma rashin aikin yi”.
Yayin da jama’a ke fargaba da kokawa kan illolin da matakin rufe kamfanin ya jawo ga tattalin ariki, shi kuwa jami’in hulda da jama’a na kamfanin na SETRACO a Najeriya, Mista Abu Malik, a wata hira da ya yi da wakilin BBC Is’haq Khalid, ya ce sun rufe kamfanin ne na wucin gadi ba na dindin-din ba a yankin na Jama’are.
’Yan kasashen wajen da aka kama ma’aikatan kamfanin na SETRACO sun hada da ’yan Lebanon biyu, da ’yan Syria biyu, da dan Burtaniya da dan Italiya da kuma dan Girka.

'Ana ci gaba da bincike'

Idan za a iya tunawa wata kungiya mai suna Jama’atu Ansarul Musulmina fi Biladil Sudan ta yi ikararin kama su saboda abin da ta kira zaluncin kasashen Yamma ga musulmi kamar a Mali da Afghanistan.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi, Hassan Muhammad Auyo, ya bayyana cewa har yanzu ana nan ana bincike a kokarin da jami’an tsaro ke yin a kubutar da mutanen.

Monday, 25 February 2013

An nuna bidiyon 'Faransawan da aka sace

 Faransawa

Wani hoton bidiyo da aka sa a shafin internet na You Tube ya nuna iyalan Faransawan nan bakwai, ciki harda 'ya'yansu da wasu 'yan bindiga suka sace a Kamaru.
Hoton bidiyon ya nuna wani mutum yana karanta jawabi a gaban maza biyu da mace daya da kuma yara hudu.
Mutanen da suka ce su 'ya'yan Jama'atu Ahlus sunna liddaa'awati wal jahad da aka fi sani da Boko Haram ne, sun nemi a saki fursunonin da ake tsare da su a Najeriya da kuma Kamaru.
Iyalan dai na zaune ne a birnin Yaounde na kasar Kamaru, inda mahaifinsu ke aiki da kamfanin gas na Faransa Suez. An sace su ne lokacin da suke komawa gida daga wurin shakatawa ba Waza National Park.
Mutumin da ke jawabi a bidiyon, ya ce "muna gaya wa shugaban Faransa cewa mu 'yan kungiyar Boko Haram ne muka kame iyalan Faransawan su bakwai".

'Matukar kaduwa'

Kungiyar ta yi barazanar za ta kashe Faransawan matukar ba a biya masu wasu bukatun su ba, da suka hada da sako wasu 'yan kungiyar da ake rike da su a gidajen kason Najeriya da Kamaru.
Sun kuma zargi shugaban Faransa Francois Hollande, da kaddamar da yaki a kan Musulunci, abin da ke nuni da yakin da dakarun Faransa ke yi a kasar Mali.
A ranar Alhamis Faransa ta ce tana da masaniyyar cewa "kungiyar Boko Haram ce ta sace mutanen", kuma an shiga da su Najeriya daga Kamarun.
"Wannan hoton abin tayar da hankali ne, kuma mun yi matukar kaduwa," a cewar ministan harkokin wajen Faransa Laurent Fabius, cikin sanarwar da ya fitar.
A makon da ya gabata ne dai wasu mutane akan babura suka sace iyalin Faransawan.
Turawan dai a cikin bidiyon, sun nuna cewa suna cikin koshin lafiya, babu kuma wata alamar tagayyara tare dasu. Wani na kusa da su ya tabbatarwa da kamfanin dillancin labarai na Faransa AFP cewa hoton na hakika ne.
An yi dai ta samun rahotanni masu karo da juna tun daga wancan lokaci game da makomar mutanen da kuma yunkurin da ake na ceto su.

An rufe jami'ar jihar Nasarawa

 

Gwamnatin jihar Nasarawa a arewacin Najeriya ta bada umarnin rufe jami'ar jihar dake garin Keffi bayan wata mummunar zanga-zanga da É—alibai suka yi suna nuna rashin jin daÉ—insu da matsalar karancin ruwa da suke fuskanta.
A lokacin zanga-zangar daliban sun toshe babban titin da ke zuwa Abuja, inda suka ƙona tayoyi.
Daga bisani kuma an tura jami'an tsaro domin tarwatsasu.
Rahotanni sunce an samu asarar rayuka bayan da jami'an tsaro suka isa wurin masu zanga zangar.
Ɗaliban dai sun ce sun yi zanga-zangar ce saboda mummunan Ƙarancin ruwan da suke fama da shi.

Friday, 22 February 2013

Bana tunanin ajiye aiki- Wenger



Kocin Arsenal Arsene Wenger ya ce bai taba tunanin ajiye aikinsa ba a wannan mako.
Arsenal dai na fuskantar kalubalen kaiwa wasan dab da kusa da na karshe a gasar zakarun Turai bayan ta sha kashi a hannun Bayern Munich a wasan kifa daya kwalla da aka yi a ranar Talata.
Kashin da ta sha a hannu Bayern din ya biyo bayan fidda ta da aka yi a gasar cin kofin FA.
"Ya kamata mu hada kai, kada mu bari korofen korofen mutanen su karya lagwan mu saboda wasa daya." In ji Wenger.
Wenger dai ya fuskancin matsin lamba a wannan makon a yayinda wasu rahotanni ke nuni da cewa yana tunanin ajiye aikinsa.
Arsenal dai ba ta lashe kofi ba tun baya da ta doke Manchester United a bugun fenarity a gasar cin kofin FA a shekarar 2005.
A wani taron manema labarai da aka yi, an tambayi Wenger ko zai ajiye aikinsa, sai ya maida martani da cewa; "ko kadan bana tunanin hakan".
"Ina da kwantaragi har zuwa shekara 2014 kuma muna cikin wani dan gejeren lokaci ne yanzu. Sai shekara ta 2014 zan yi tunani abun da zan yi idan kwantaragi na ya kare".

Barack Obama ya kara tura sojoji zuwa Nijar

Mahamadou Isoufu-Shugaban Nijar

Shugaban Amurka, Barrack Obama ya kara tura wasu sojojin Amurka 40 zuwa Jamhuriyar Niger, domin taimakawa wajen tattara bayanan sirri
Hakan na faruwa a daidai lokacin da sojojin Faransa tare da hadin guiwar sojojin wasu kasashen Africa ke ci gaba da fafatawa da kungiyoyin 'yan tawaye masu kishin islama a kasar Mali.

Fadar White House ce dai ta bayyana haka, a wata wasika data turawa majalissar dokokin Amurkar.
Sojojin Amurkar zasu bi sahun takwarorinsu 60 ne wadanda dama can Amurka ta tura zuwa Jamhuriyar ta Niger.
Kamar yadda wasikar ta bayyana, an tura sojojin ne ranar larabar da ta wuce.
Dama a can baya, wani jami'in Amurka ya ce ma'aiakatar tsaron Amurkar na shirin girke jiragen da basa amfani da direbobi, mai yiwa a Jamhuriyar Niger, domin taimakawa wajen tattara bayanai akan kungiyar Al-Qaeda a yankin Maghreb da kuma abokan kawancenta a yankin.

Kotu ta bayar da belin Oscar Pistorius

Oscar Pistorius 
 
Oscar Pistorius ya ce a bisa kuskure ne ya kashe Reeva Steenkamp.
 
An bayar da belin dan tseren Afrika ta Kudu Oscar Pistorius, wanda ake tuhuma da kisan budurwarsa, bayan wani dogon zaman jin bahasi.
Dan tseren wasan nakasassun ya musanta kisan, yana mai cewa ya harbe Reeva Steenkamp ne bayan da yayi zaton cewa wani ne ya shiga gidansa ba tare da izini ba.

Sharadn belin sun hada da ya rinka mika kansa ga jami'an 'yan sanda sau biyu a kowanne mako.
Zai biya kudin beli dala 113,000 wato miliyan daya na kudin Rand na Afrika ta Kudu, tare da mutanen da za su tsaya masa.
Sannan za a kwace dukkan makaman da ya mallaka tare da hana shi shan giya, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito.
Masu gabatar da kara sun nemi kada a bayar da belinsa saboda akwai yiwuwar Mr Pistorius, mai shekaru 26, zai gudu.
Sai dai mai shari'a Desmond Nair ya ce bai gamsu cewa dan wasan zai gudu ba, ko kuma cewa mutum ne mai son tashin hankali.

Sakamakon wasannin Kofin Europa

 'yan Chelsea

An kammala wasannin zagaye na biyu na cin Kofin kwallon kafa na Europa tsakanin kungiyoyi 32 a kasashe daban-daban inda mai rike da kofi Atletico Madrid ta yi waje.
A karshen wasannin an samu kungiyoyi 16 da zasu fafata domin neman zuwa matakin wasan gab da na kusa da karshe.

Mai rike da Kofin Atletico Madrid ta yi waje a gasar a hannun Rubin Kazan.
Ga yadda sakamakon ya kasance
1-Met's kharkiv 0-1 Newcastle Jumulla (0-1)
2-Lyon 1-1 Tottenham Jumulla (2-3)
3-Chelsea1- 1Sparta Prague (2-1)
4-Liverpool 3-1 Zenit St Petersburg (3-3)
5- Rubin Kazan 0-1 Atl Madrid (2-1)
6- CFR Cluj-Napoca 0-3 interMilan (0-5)
7- Dnipro 1-1 FC Basel (1-3)
8- Genk 0-2 VfB Stuttgard (1-3)
9- Lazio 2-0 Borussia M'gladbach (5-3)
10- Benfica 2 - 1 B Leverkusen (3-1)
11- Bordaeux 1 -0 Dynamo Kiev (2-1)
12- Fenerbahce 1 -0 Bate Borisov (1-0)
13- Viktoria Plzen 2-2 Napoli (5-0)
14- Steau Bucuresti 2-0 Ajax (4-2)
15- Olympiakos Piraeus 0-1 Levante (0-4)
16- Hannover 96 1-1 Anzhi (2-4)

Barcelona za ta yi wasa da Isra'ila

lionel messi

Shugaban kasar Isra'ila da shugaban Kulab din Barcelona sun bayyana cewa suna shirya wani wasa tsakanin kungiyar kwallon kafa ta hadin-gwiwa tsakanin yahudawa da Palasdinawa da kuma Barcelona
Za a kara ne a karshen watan Yuli a dandalin Ramat Gan da ke Isra'ila.

Irin kauna da goyon bayan da ake yi wa Barcelona suka sa hada kan Palasdinawa da Yahudawa magoya bayan kulab din da ke bangarori biyun da ke fada da juna.
Shugaban kulab din wanda ke wata ziyara a Isra'ila da kuma gabar yammacin kogin Jordan a karon farko ya bayyana cewa kulab din na so ya yaukaka dankon zumunci tare da wanzar da zaman lafiya da lumana a yankin ta hanyar wasan kwallon kafa.
Ba a dai san ko su wa da wa za a ayyana sunayensu a matsayin wadanda za su taka ledar ba, amma ana sa ran manyan 'yan wasan Palasdinawa da yahudawa ne za su shiga wasan, inda za su kara da 'yan Barcelonan.
Ana dai sa ran gwarzon na 'yan wasan kwallon kafa Lionel Messi na daga cikin wadanda za su kai ziyara can.
A bara dai harkar siyasar Gabas-ta-tsakiya ta shafi kulab din na Barcelona.
Saboda ta karrama wani tsohon sojan kasar Isra'ila, Gilad Shalit, wanda masu fafitikar Palasdinawa suka tsare shi shekara biyar ta hanyar gayyatarsa a matsayin bako na musamman don ya kalli wasan da ta yi da Real Madrid, a Nuo Camp.
Wannan ya bata wa Palasdinawa rai, amma daga baya Kungiyar Barcan ta gayyaci wani tsohon dan wasan kwallon kafa a yankin Palasdinawa, wanda kasar Isra'ila ta tsare tsawon shekara uku a matsayin bako na musamman zuwa kallon wani wasanta, amma bai amsa gayyatar ba.

An kashe mutane tara a Filato

 

Rahotanni daga jihar Filaton Najeriya na cewa 'yan bindiga da a ba san ko su wanene ba sun kashe mutane tara a harin da suka kai a yankin Vom a ranar Alhamis da daddare.
Sai dai kwamishinan 'yan sandan jihar, Mista Chris Olakpe, ya shaidawa BBC cewa gawarwakin mutane hudu suka gano.

Jihar Filato dai ta dade tana fama da rikice-rikicen da suke da dangantaka da kabilanci da addini da kuma siyasa.

Karar harbe-harbe a Maiduguri

Rahotanni daga Maiduguri, babban birnin jihar Borno, na cewa an shafe daren ranar Alhamis ana jin karar harbe-harben bindigogi a sassa daban-daban na birnin.
Sai dai har yanzu ba a san ko wannan lamari ya yi sanadiyar mutuwa ko jikkata mutane ba.
Ko a ranar Laraba ma , akalla mutane takwas ne suka mutu sanadiyar fashewar wani abu da ake zaton bam ne a unguwar Kwastan da ke birnin.
Haka kuma shaidu sun ce bakin hayaki ya turnike sararin samaniya, kuma shaguna da dama sun kone.

Ba za mu biya diyya a Haiti ba — Ban Ki Moon

 

Majalisar Dinkin Duniya ta yi watsi da bukatar da 'yan kasar Haiti suka yi cewa ta ba su diyya bayan da suka kamu da cutar amai da gudawa.
Ana zargin dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar da ke aiki a Haiti, da kai kwayoyin cutar amai da gudawa kasar, lamarin da ya sanya fiye da mutane 600, 000 suka kamu da ita.
Kimanin mutane 8000 sun mutu sakamakon lamarin tun daga shekarar 2010.
A wata sanarwa da kakakin Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki Moon, ya fitar ya ce wani kuduri da babban taron Majalisar ya amince da shi ya ba ta kariya daga biyan diyya ga 'yan kasar ta Haiti.
Majalisar ta ki amincewa da aikata laifi duk da cewa wadansu shaidu sun nuna ma'aikatanta ne 'yan asalin kasar Nepal suka yi sanadiyar barkewar cutar sakamakon zubar da sharar da su ka yi a wani kogi na kasar ta Haiti.
Wani lauyan mutanen ya shaidawa BBC cewa za su nufi babbar kotun kasar don ganin an tilastawa Majalisar biyan diyya.

Morsi yana so a gudanar da zabe a Masar

 

Shugaban kasar Masar, Mohammed Morsi, ya yi kira da a fara gudanar da zaben majalisun dokoki daga karshen watan Aprilu mai zuwa.
Wata sanarwa da shugaban kasar ya fitar ta ce za a fara zaben ne daga ranar 27 ga watan Aprilu, a kammala a karshen watan Yuni.
Sanarwar ta ce za a gudanar da zabukan ne a matakai gudu hudu, kuma daga yanki zuwa yanki.
Za a gudanar da zaben ne daki-daki a yankuna daban-daban ne saboda karancin masu sanya idanu a kan zabe.

Thursday, 21 February 2013

Kila-wa-kala game da makomar Faransawa da aka sace

Taswirar Kamaru

Gwamnatocin Faransa da Nijeriya sun musanta wasu rahotanni da ke cewar an gano Faransawar nan bakwai da aka yi awon gaba dasu a arewacin Kamaru.
Tun farko dai, Ministan kula da 'yan mazan jiya na kasar Faransa ya bayayna a gaban majalissar dokokin Faransa cewa an gano Faransawan a wani gari a arewacin Nigeria, amma daga bisani ya janye maganarsa yana mai cewar babu wani tabbasci a kan labarin.
An dai yi ta samu rahotanni masu karo da juna a kan al'amarin, inda wata majiya ta sojojin Kamaru ita ma ta ce an gano Faransawan.
Rahotanni na baya baya na cewa an gano inda ake rike da Faransawar, kuma jami'an tsaro sun kewaye wurin, sai dai babu wata majiyar tsaro da ta tabbatar da gaskiyar hakan ya zuwa yanzu.

Shari'ar Pistorius: An nada sabon jami'in dan sanda

 Pistorius

An sauya jami'in dan sandan da ke jagorantar binciken kisan kan da ake zargin Oscar Pistorius da shi, bayan da ta bayyana cewar shi kansa ya na fuskantar tuhume-tuhume bakwai na kokarin aikata kisan kai, shekaru biyun da suka wuce.
Kwamishinar 'yan sanda ta kasa a Afrika ta Kudu, Mangwashi Victoria Phiyega ce ta bayar da sanarwar inda tace 'Na yanke shawarar wannan muhimmin batu , wannan muhimmin bincike a karkashin shugabanci da jagorancin Kwamishin gunduma kan ayyukan bincike, Lt Janar Moonoo'.
Shi dai dan tseren, Oscar Pistorius, ana zarginsa ne da kashe budurwarsa, Reeva Steenkamp.
A gobe Juma'a, ake sa ran za a yanke hukunci game da shari'ar neman belin da aka shigar kan Mr Pistorius.

Akalla mutane 8 sun halaka a Maiduguri

 MD Abubakar, babban Spetan 'yan sandan Najeriya

Rahotanni daga Maiduguri, babban birnin jihar Borno na cewa, akalla mutane takwas ne su ka mutu sanadiyar fashewar wani abu da ake kyautata zaton bam ne a unguwar kwastan.
Bakin hayaki ya turnike sararin samania kamar yadda shaidun gani da iddo su ka tabbatar, tare da cewa Shaguna da dama da su ka kone.
Wasu magidanta a Maidugurin sun tabbatar wa da cewa sun ga gawawwakin mutane a kwance.
Wannan al'amari dai ya kara janyo zaman zulumi a birnin.
Ko a ranar laraba ma dai, wasu mutane uku sun mutu bayan fashewar wani abu a birnin Maidugurin.

Za a gabatar da shaidu a shari'ar Pistorius

 Oscar Pistorius

A ranar ta biyu a shari'ar da ake yi game da zargin kisan da ake wa Oscar Pistorius, kotu za ta cigaba da sauraron bayanai daga masu shigar da kara.
Ana tuhumar zakaran wasan tseren nakasassun ne da harbin budurwar sa, Reeva Steenkamp lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar ta, a makon jiya.
Ana sa ran jin bayanai da za su karyata wadanda Mista Pistorius ya gabatar a ranar farko.
Shi dai Pistorius ya musanta cewa ya kashe budurwarsa, wacce aka harbe a gidansa ranar Alhamis.
A wata sanarwa da ya fitar, ya ce ya yi tsammanin barawo ya kashe a lokacin da ya yi harbin.
Sai dai a zaman farko da kotun ta yi, mai shari'ar ta ce za ta saurari karar ne a matsayin wadda aka yi kisan kai da gangan.
Kotun wacce ke birnin Pretoria za ta saurari bukatar yiwuwar ba da belin Mista Pistorius, a rana ta biyu da ake gudanar da sharia a kansa.
Dan wasan dai ya musanta zargin da ake yi masa.

An kama wanda ake zargi da cacar kwallo kafa a italia

 Shugaban hukumar 'yan sandan kasa da kasa Ronald Noble

Wani da ake zargi da hannu wajen cogen wasan kwallon kafa na kasa da kasa ya shiga hannun jami'an tsaro a Italiya.
An damke shi ne a lokacin da ya isa Italiya daga Singapore, inda ya mika kansa ga 'yan sanda.

Kafofin yada labaran Italiya sun bayyana sunan mutumin da Admir Sulic.
Hukumar 'yan sanda ta kasa da kasa tace an yi imanin cewa, wanda ake zargin yana da alaka da wata kungiya dake hada cogen wasan kwallo dake Singapore.
Hukumar ta yi imanin cewa Mr. Sulic na da alaka da kungiyar cogen wasan kwallon, wanda wani dan kasuwan Singapore Tan Seet Eng da aka fi sani da Dan Tan ke da ita.
Masu bincike dai na sukar Singapore game da abin da suka kira, barin mai cacar wasanni ya zauna a kasar, ba tare da wata tsangwama ba.
Rahotannin fari dai sun nuna cewa shi ma Mr. Tan yana cikin jirgin da ya taho daga Singapore ya sauka a Italiyan.

Ambaliyar ruwa a kaduna



A Najeriya, mutanen da ambaliyar ruwa ta raba da gidajensu, na ci gaba da komawa gidajen duk da yake hukumomi sun yi gargadi game da hakan.
A cewar mutanen, talauci da rashin samun mutsuguni ne suka sanya su koma gidajen nasu bayan ruwa ya janye daga gidajen.
Wadansu mutane da suka koma gidajen na su a jihar Kaduna, sun shaidawa cewa ba za su fice daga gidajen ba, sai gwamnati ta samar mu su da sababbin gidaje.
Hukumar bayar da agajin gaggawa, NEMA ta yi kira ga mutanen da su guji komawa gidajen na su saboda hasashen da aka gudanar a bana, ya nuna cewa za a samu ruwan sama mai karfin gaske, wanda zai iya yin mummunar barna.

Shugaban facebook dan abokan aikinsa sun gana da yan jaridu


Wadansu attajiran da ke da hannun jari a harkar intanet ciki har da mutumin da ya samar da shafin facebook, Mark Zukerberg, sun sanya gasa mafi girma a fannin kimiyya.
An sanya gasar ce saboda nuna irin gudunmawar da masu nazarin kimayya suka bayar a duniya da zummar karfafawa matasa gwiwa don su karanta fannin.


Za a ware mutane biyar da suka fi yin fice a fannin kimiya a duk shekara, sannan a ba kowane kyautar da ta kai dala miliyan uku.
A cewar Mark Zukerberg, yin hakan zai sanya duniya ta sani cewa ba wai kawai shahararrun 'yan wasan kwallo da taurarin fina-finai ne kadai ke taka rawa a duniya ba, har ma da masu nazarin kimiyya.

Abin alfahari

Kudin da za a bai wa wanda ya lashe gasar ya ninka kudin da ake bai wa mutumin da ya lashe kyautar Nobel.
Kowa na iya shiga gasar sai dai manufar ita ce a karrama masana kimiyyar da ke tashe yanzu, ba wadanda suka gaba ce su ba.
Ana kallon hadin gwiwar da wadannan 'yan kasuwa suka yi a matsayin wani abin alfahari idan aka yi la'akari da yadda suke zafafa gasa a tsakanisu kan yadda kowanne zai fi dan uwansa karbuwa a fannin intanet.
Mark Zukerberg ya ce 'yan jarida ne kawai ke kambama rashin jituwar da ke tsakanin google da facebook da kuma apple .
A bana dai, an bai wa wadansu masu nazarin kimiyya su goma sha daya kyautar dala miliyan uku-uku, saboda binciken da suka yi a kan dalilan da ke kawo cutar daji, da ciwon sukari da maganin cututtukan da kuma inganta rayuwa dan adam.

Mexico ba ta yi bincike kan mutanen da suka bata ba


Kungiyar kare hakkin dan adam, Human Rights Watch, ta ce Mexico ta gaza yin bincike don gano dubban mutanen da suka yi batan-dabo karkashin mulkin tsohon shugaba Felipe Calderon.
Kungiyar ta zargi dukkanin jami'an tsaron kasar da hannu wajen bacewar mutanen, tana mai cewa masu safarar miyagun kwayoyi ne ke sanyawa mutane na bacewa.
Wadansu alkaluman gwamnati da aka tseguntawa 'yan jarida a shekarar 2012, sun nuna cewa mutanen da suka bata a kasar sun kai dubu 25, 000.
Kungiyar ta yi kira ga gwamnatin shugaba Enrique Pena Nieto ta gaggawa shawo kan matsalar.
Gabanin fitar da rahoton na Human Rights Watch dai, ministan harkokin cikin gida na Mexico, Miguel Angel Osorio, ya yi wata tattaunawa da kungiyar, sannan ya yi alkawarin daukar matakan gaggauwa, wadanda suka hada da samar da hukumar da za ta gano gawawwakin mutanen da suka bata.

Wednesday, 20 February 2013

AC Milan ta casa Barca

ac milan barcelona

Kungiyar AC Milan ta Italiya ta lallasa Barcelona ta Spaniya da ci 2-0 a wasan cin Kofin Zakarun Turai.
Wannan karawar farko ce ta kungiyoyi 16 wadda bayan karawa ta biyu za a fitar da guda 8 da za su yi wasan gab da na kusa da karshe.
Boateng ne ya fara jefa kwallo a ragar Barcelona a minti na 57, kafin minti na 81 kuma Sule Muntari ya kara ta biyun.
A daya wasan na cin Kofin na Zakarun Turai, Galatasaray ta Turkiyya ta yi 1-1 da Schalke 04 ta Jamus.
Yilmaz ne ya ci wa Galatasaray kwallonta a na minti 12 da fara wasa.
Ana gab da tafiya hutun rabin lokaci a minti na 45 Jones ya rama wa bakin .
A ranar 12 ga watan Maris ne za ayi karo na biyu na wasannin.

Man U : Gill zai sauka daga shugabanci

david gill

Kungiyar Manchester United ta tabbatar cewa David Gill zai sauka daga shugabancinta a ranar 30 ga watan Yuni.
Sa dai Gill dan shekara 55 wanda ya fara aiki da klub din a watan Fabrairu na 1997 a matsayin darektan kudi kafin ya zama shugaba a 2003 zai ci gaba da zama a matsayin darekta a kungiyar.


Mataimakinsa Ed Woodward shi ne zai dare kujerarsa.
Gill ya ce matakin da ya dauka na sauka daga shugabancin da maye gurbinsa da Woodward zai taimaka wajen sabunta klub din kamar yadda ya ambata.
Kocin kungiyar Sir Alex Ferguson bai ji dadin shawarar da Gill din ya yanke ba ta ajiye mukamin nasa.
Ya ce ''babbar asara ce a wurina amma tun da zai ci gaba da zama a hukumar kungiyar hakan zai karfafa min guiwa.''
Sir Alex ya kara da cewa ''idan da zan iya shawo kansa ya sauya shawara da sai na yi, to amma ya riga ya yanke hukunci kuma ina mutunta shi a kan hakan.''
A karkashin shugabancin Gill din ribar da Manchester United ta ke samu ta karu zuwa kashi 74 cikin dari a watanni shidan karshe na 2012.
Amma kuma ana bin klub din bashin fam miliyan 366.6 kuma kudaden da a ke kashewa 'yan wasa da ma'aikata ya karu da sama da kashi 10 cikin dari.

Shugaban Alkalan Kenya na fuskantar barazana

 Kenya

Shugaban alkalan kasar Kenya ya ce yana fuskantar barazana gabanin zaben shugaban kasa da na 'yan majalisun kasar da za a yi a watan gobe.
A wata sanarwa da ya aikewa manema labarai, babban mai shari'a Willy Mutunga, ya ce ya samu sakon barazana a wata wasika da kungiyar 'yan daba ta Mungiki ta aike masa.
Ya ce wasikar ta gargade shi kan kada ya haramtawa da daya daga cikin 'yan takarar shugaban kasar Uhuru Kenyatta, shiga zaben na watan gobe.
Wakilin BBC ya ce ana yiwa Alkalin Alkalan kallon wani mutum da ke kokarin kawo sauyi a fannin shari'ar kasar - wanda ke cike da cin hanci da rashawa. Kuma za su taka rawa sosai a zaben na watan gobe.
A makon da ya gabata ma yayi korafin cewa wani jami'in shige da fice, ya yi kokarin hana shi hawa jirgi domin fita kasar waje, har sai ya nemi izini daga shugaban shugaban ma'aikatan kasar.



'Yan bindiga a Najeriya sun sace 'yan Kasashen waje a Bayelsa

Mohammed Abubakar Babban Spetan 'yan sandan Najeriya

Wasu 'yan bindiga a Najeriya sun sake sace ma'aikata 'yan kasashen waje shida.
'Yan sanda sun ce maharan sun shiga cikin wani jirgin ruwan daukar mai ne a gabar ruwan Bayelsa ranar Lahadi.
Mutanen da aka kama sun fito ne daga kasashen Ukraine, India da kuma Rasha.
Hukumar SSS a Najeriya ta yi kame
A wani bangaren kuma Hukumar Leken Asiri ta kasar SSS, ta cafke wani mutum mai kimanin shekarau 50 mai suna Abdullahi Mustapha Berende dan asalin jihar Kwara, da take zargin da hannu wajen aikata laifin leken asiri da ta'addanci a kasa, tare da hadin gwiwar wasu 'yan kasar Iran.
Hukumar ta SSS din ta kuma ce a bisa bincike, da sa idon da ta dade tana yi, wanda ake zargin ya sha yin tafiye-tafiye zuwa kasar Iran, domin tattaunawa da wasu Iraniyawan da suka dade suna jagorancin wata kungiyar 'yan ta'adda ta kasa da kasa, da yanzu haka ke yunkurin cimma wasu manufofi a Najeriyar

Wata Kungiyar kabilar Igbo ta ayyana kafa Jamhuriyar Biafra

 Wasu masu fafautikar kafa Biafra da tutucin kasar

Kungiyar nan mai suna Biafra Zionist Movement mai fafutikar kafa kasar yan kabilar Igbo zalla a Najeriya ta kaddamar da abun da ta kira ''Gwamnatin jamhuriyyar Biafra'' a birnin Enugu.
Kungiyar ta ambata sunayen wasu fitattun 'yan kabilar Igbo da ke rike da manyan mukamai a gwamnatin Najeriya, kamar su Cif Anyim Pius Anyim da Ngozi Okonjo-Iweala da Dezanie Allison Madueke a matsayin kusoshin gwamnatinta.
Kungiyar ta bukaci wadannan mutane da su karbi mukaman nan da mako guda, haka kuma ta umurci jami'an tsaron tarayyar Najeriya da su kwashe ya -nasu - ya -nasu su fice daga yankin nan da makunni biyu masu zuwa.
A watan Nuwamban bara ne dai wannan kungiya ta bayyana kafuwar jamhuriyar, al'amarin da ya sa rundunar 'yan sandan jihar Enugu ta kame shugabanni da 'ya'yan kungiyar fiye da dari daya. Kuma ta gurfanar da su a kotu, amma daga baya aka sako su a matsayin beli.

An manna kasidun musanta tsagaita wuta

 Shugaban kungiyar Boko Haram, Imam Abubakar Shekau

Al'ummar Maiduguri a jihar Borno da ke arewacin Najeriya, sun wayi gari da wasu kasidu manne a jikin massallatai da turakun wutar lantarki.
Takardun na dauke da sakon da ke cewa, sun fito ne daga jagoran kungiyar Jama'atu Ahlussunah Lidda'awati wal jihad da aka fi sani Boko Haram, Imam Abubakar Shakau.
Sakon dai ya yi watsi da maganar tsagaita bude wuta, da wani wanda ya ce yana magana da yawun shugaban kungiyar ya yi, a baya-bayan nan.
Wasu al'ummomin birnin sun ce tun a yammacin ranar Talata ne suka samu kasidun da aka rarraba, ko aka lika a unguwanni daban-daban na birnin.
Sai dai kwamishinan yada labarai na jihar Borno, Inuwa Buwala yace bashi da masaniya a kan hakan, amma yana bincike.
Gwamnatin jihar Borno ce ta yi ikirarin cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da mutumin da ya yi ikirarin magana da yawun shugaban kungiyar ta Boko Haram.
Ita dai kungiyar a yawancin lokuta takan fitar da sanarwa ne ta hanyar sako na Email, ko hira da 'yan jaridu ta waya, ko kuma sakon bidiyo a shafin Youtube na intanet.
Sai dai a lokuta da dama a baya ma, Boko Haram ta fitar da sakonni ta hanyar lillika kasidu a wasu wurare .

'An ji ihu da harbi a gidan Pistorius'

 Oscar Pistorius


Wani mai bada shaida a shari'ar da ake game da zargin kisan da ake wa Oscar Pistorius, ya ce ya ji ihu da harbe-harbe a gidan dan wasan.
Jami'in dan sandan da ya bayyana hakan, ya ce hakan ya faru ne a daren da aka kashe Reeva Steenkamp.
A rana ta biyu na shari'ar da ake yi a Pretoria, game da bada belin Mr. Pistorius, dan sandan ya ce zakaran wasan zai iya tsere wa.
Shi dai Oscar ya musanta zargin da ake masa na kisan Reeva da gangan.
Masu gabatar da karar sun kuma ce, an ji ana fada a gidan Oscar da misalin karfe biyu zuwa uku na daren da lamarin ya auku.
Jami'in dan sandan da ya fara isa gidan Oscar, Mr Botha ya ce suna da rahoton dan sanda , wanda wani shaida yace ya ji muryar mace tana ta ihu sannan kuma ya ji harbi fiye da sau daya daga gidan Mr. Pistorius.
Sai dai Mr. Pistorius ya ce basu yi fada da Reeva ba, kuma ya yi barci har kusan gaf da lokacin da aka ji harbin.

Tuesday, 19 February 2013

Afghanistan: Farar hula da ke mutuwa na raguwa

 Hamid Karzai

Wani rahoto da Majalisar Dinkin Duniya ta fitar ya nuna cewa a karo na farko a cikin shekaru shida yawan fararen hular da tashe-tashen hankulan Afghanistan ke rutsawa da su ya ragu.
Sai dai kuma ko da yake adadin daukacin fararen hular da al’amarin ke shafa ya ragu a shekarar 2012, adadin wadanda ke jikkata ya dan karu.

Raguwar fararen hular da ke mutuwa da kashi goma sha biyu cikin dari dai na nuni da cewa Afghanistan ta kama hanyar zama wani wuri da mutanen da ba mayaka ba ne ke da aminci.
Rahoton, wanda Hukumar Agazawa Afghansitan ta Majalisar Dinkin Duniya ta wallafa, ya nuna cewa masu tayar da kayar baya ne suka haddasa mutuwar ko raunata kashi tamanin cikin dari na wadanda tashe-tashen hankulan kan shafa, kuma yawan kisan gillar da kungiyar Taliban ke aikatawa ya karu matuka.
Mutuwar fararen hula dai al'amari ne mai sarkakiya a siyasar Afghanistan; kuma yawan fararen hular da ke mutuwa sakamakon ayyukan rundunar kungiyar tsaro ta NATO da dakarun Afghanistan ya ragu sosai.
Wannan labari dai mai dadin ji ne ga dakarun kasashen waje, wadanda ke fuskantar matsin lamba daga gwamnati a makon da ya gabata a kan su takaita kai hare-hare da jiragen saman yaki a yankunan da fararen hula ke zaune.

Pistorius ya 'harbe budurwarsa a bandaki

 Oscar Pistorius a Kotu

Zakaran dan wasan tseren nakassasun nan, Oscar Pistorius ya harbi budurwarsa Reeva Steenkamp sau uku a lokacin da take bandaki, a cewar masu gabatar da kara.
Ana kara samun bayanai game da kisan Reeva ne, a zaman kotun da ake ayi rnar Talata a Afirka ta Kudu, inda za a duba yiwuwar daba bellin Oscar.

Pistorius ya fashe da kuka a yayin da ya ji tuhumar da ake masa na kisan budurwarsa da gangan, amma lauyansa ya shaida wa kotu cewa bai aikata kisan kai ba.
Zaman kotun da ake yi Pretoria na zuwa ne a rana daya da jana'izar Reeva a Port Elizabeth.
Mai shigar da kara Gerrie Nel ya bayyana wa kotun cewa, a daren da lamarin ya auku, Oscar wanda bashi da kafafuwa ya sanya kafafuwan karfensa kuma ya yi tafiya na mita bakwai, sannan ya harbi kyauren bandakinsa.
Ya yi harbi sau hudu, inda ya samu Steenkamp sau uku, kuma daga bisani ya balla kyauren bandakin ya dauke ta ya kaita kasa, Inji Mr. Nel.
Sai dai lauya mai kare wanda ake kara, Barry Roux ya shaida wa kotu cewa, zakaran wasan bashi da masaniyar cewa tana bandakin, kafin yayi harbin.
Saboda haka masu gabatar da karar basu da wata shedar cewa da gangan ya kashe ta, don haka bai aikata kisan kai ba.

'Yan PDP na son shiga APC —Shekarau

 Malam Ibrahim Shekarau

Tsohon Gwamnan Jihar Kano a arewacin Najeriya, Malam Ibrahim Shekarau, ya ce wadansu manyan jami’an jam’iyyar PDP mai mulkin kasar sun fara nuna sha’awar shiga sabuwar jam’iyyar APC.
A cewarsa, “A daidaku, ba gwamnoni na PDP kawai ba, akwai wasu daga cikin jami’ai ko ’ya’yan jam’iyyar PDP wadanda suka fara tuntubar mu [da] cewa suna da sha’awa su shigo cikin wannan tsari, kuma muka ce kofar mu a bude take”.

Sai dai kuma, tsohon gwamnan ya ce yana ganin da dama daga cikinsu za su jira su ga “ta gama nuna” kafin su bayyana abin da ke zukatansu.
Mai baiwa shugaban kasa shawar kan harkokin siyasa, Ahmed Gulak ya ce, Shugaba Goodluck Jonathan nada masaniyar cewa wasu gwamnoni a kasar na yiwa PDP zagon kasa saboda su cimma bukatunsu.
Gulak a wata hira da yayi da wani gidan talabijin a kasar ya ce, gwamnonin ba za su yi narasa ba.
Shima Malam shekarau a wata hira da ya yi , lokacin da ya kai ziyara ofishinmu da ke London, ya ce suna sane da rahotannin da ke cewa ana kokarin amfani da wadansu bara-gurbi domin kawo tsaiko a tafiyar ’yan adawar.
“Mun ga wadannan zarge-zarge a kafafen yada labarai, kuma mun kirawo wadanda wannan zargi ya fada kansu sun tabbatar mana cewa babu gaskiya, wannan yarfe ne na siyasa…”.
*Masu saurare za su iya jin cikakkiyar hirar ranar Asabar 23 ga wata a filinmu na Gane Mani Hanya a Shirinmu na Safe wanda ke zuwa da karfe shida da rabi agogon Najeriya da Nijar a kan mita 25, da 41 da kuma 49.

Monday, 18 February 2013

Sakamakon farko-farko na zaben shugaban kasar da aka gudanar ranar Lahadi a Ecuador ya nuna cewa Shugaba Rafael Correa ya yi nasarar samun damar ci gaba da rike mukaminsa.
Adadin kuri’un da dama aka yi hasashen shugaban kasar mai ra’ayin gurguzu zai samu ya kai yadda ba sai an je zagaye na biyu ba kuma tuni ma dai abokan hamayyarsa suka amince da shan kaye.

David Cameron ya ziyaraci India

 David Cameron a India

Firayim Ministan Burtaniya David Cameron ya sauka a India, inda zai jagoranci wani yunkuri na biyu na habaka cinikayya bayan wata ziyara da ya kai a shekarar 2010.
Mista Cameron na jagorantar wata babbar tawaga ta ’yan kasuwar Burtaniya wadanda za su duba hanyoyin cin moriyar tattalin arzikin kasar India wanda shi ne na biyu a duniya wajen bunkasa cikin hanzari.

Ita ma kasar ta India yanzu ta zama babbar mai zuba jari a Burtaniya.
India dai na cikin kasashen da David Cameron ya fara kaiwa ziyara jim kadan bayan ya zama Firayim Minista a shekarar 2010.
Kafin ziyarar tasa ya ce yana so dangantakar Burtaniya da India ta zama daya daga cikin manya-manyan kawancen karni na ashirin da daya. Yana kuma fata kamfanonin Burtaniya za su samu muhimman kwangiloli a kasar ta India.
Mista Cameron na kuma zawarcin karin daliban India su je su yi karatu a jami'o'in Burtaniya, amma kuma Indiyawa da dama na ganin hakan ba zai yiwu ba saboda tsauraran ka’idojin bayar da izinin shiga kasar wato visa.
Sai dai kuma Mista Cameron zai yi kokarin kawar da wannan fargaba: kafin fara ziyarar tasa ya ce ba za a kayyade adadin dalibai ’yan India da za su iya zuwa Burtaniya karatu ba.
Firayim Ministan yana kuma fatan zai iya gamsar da jama’a cewa Burtaniya ta fi ko wacce kasa dacewa da cinikayya da India.

Farautar barayin 'yan kasashen waje

 


Jami’an tsaro a Najeriya sun ce suna farautar wadanda suka sace ma’aikatan wani kamfanin gine-gine ’yan kasashen waje su bakwai.
An sace ma’aikatan ne masu aiki da kamfanin Setraco mallakar ’yan kasar Lebanon a garin Jama’are na Jihar Bauchi dake arewa maso gabashin kasar.


An bayyana cewa wadanda aka sacen a abin da ake ganin satar mutane mafi girma a arewacin Najeriya a dan tsakanin nan, sun hada da dan kasar Italiya, da dan kasar Philippines, da dan kasar Burtaniya, da dan kasar Girka da kuma ’yan kasar Labanon.
Wakilin BBC a Jihar ta Bauchi ya ce maharani sun datse hanyar zuwa gidan da mutane suke, sannan suka kai hari a kan ofishin ’yansanda na yankin da gidan yari—ko da yake ba su kubutar da fursunoni ba.
Maharan, a cewar wakilin na BBC, Is'haq Khalid, sun shiga cikin gidan kwanan ma’ikatan dake wani wuri da ake kira Life Camp ne ta hanyar fasa ginin da bama-bamai daga ta baya, suka kashe mai gadi É—aya, sannan suka sace mutanen.
Kwamishinan ’yan sandan Jihar ta Bauchi, Alhaji Abubakar Ladan, ya tabbatar da sace ’yan Æ™asashen wajen bakwai.

Babu asarar rai ko jikkata

Kwaminishinan ya kuma tabbatar da kai hari a kan ofishin ’yan sandan dake kusa da wajen amma ya ce babu asarar rai ko jikkkata sai dai an Æ™ona motocin yan sanda guda biyu.
Shi dai kamfanin na Setraco, kamfanin gine-gine ne mai hedikwata a Abuja, yana kuma ayyukan kwangiloli musamman na gina hanyoyin mota a Najeriya, kuma ma’aikatansa sun hada da ’yan Nijeriya da ’yan kasashen waje.
Har yanzu ’yan sanda ba su gano ko su waye suka kai harin ba, kuma babu wata kungiya da ta dauki alhakin sace mutanen.
A Najeriya dai an sha samun sace-sacen mutane ’yan Æ™asashen waje, inda a wadansu lokutan akan yi garkuwa da su domin neman kuÉ—in fansa.

Saturday, 16 February 2013

Ministocin kasashe 20 za su gana a Moscow

 Shugabannin kasashen G20

Ministocin kudi daga kasashen duniya ashirin masu karfin tattalin arziki, wato G20, za su gana a Moscow.
Yayin ganawar, ministocin za su tattauna a kan wani yunkuri na yin kwaskwarima ga ka'idojin biyan haraji wadanda ke baiwa manyan kamfanoni damar kaucewa biyan harajin.
Birtaniya, da Jamus, da Faransa ne ke jagorantar yunkurin na daukar matakin ba-sani-ba-sabo a kan manyan kamfanonin kasa-da-kasa masu kaucewa biyan haraji ta hanyar karkatar da ribar da suke samu zuwa kasashen da suke da hedkwata, inda ake yi musu rangwamen haraji.
Yunkurin dai na zuwa ne yayin da muhawara ta yi zafi a Birtaniya bayan ta bayyana cewa manyan kamfanoni irinsu Google, da Amazon, da Starbucks na biyan harajin da bai taka kara ya karya ba idan aka kawatanta da dimbin kudin shigar da suke samu a kasar ta Birtaniya.

Harbin bindiga ne ajalin Dorner —jami'ai

 Christopher Dorner

Jami'ai a Jihar California ta Amurka sun ce dan sandan nan da aka yi ta farautarsa wanda aka samu gawarsa a kone a tsaunukan Los Angeles ya mutu ne sakamakon raunin da ya yi a ka.
Wani binciken da likitoci suka gudanar a kan gawar Christopher Dorner ya nuna cewa raunin da ya yi a ka sakamakon wani harbi daya na bindiga ne ya yi ajalinsa.

Sai dai kuma babban jami'in 'yan sanda na yankin San Bernadino, wanda ya bayar da sanarwar sakamakon binciken yayin wani taron manema labarai, ya ce ba a iya tantancewa ba ko Dorner ne ya habe kansa ko harbe shi aka yi.
A makon da ya gabata ne dai tsohon jami'in dan sandan na birnin Los Angeles ya ranta a na kare bayan an zarge shi da kisan mutane uku—ciki har da dan sanda daya—da kuma jikkata wasu mutanen uku.
Wani dan sandan kuma ya rasa ransa kafin gobara ta tashi ta kuma kone dakin da Dorner ya buya a tsaunukan Los Angels.
Dorner ya wallafa wata sanarwa mai daga hankali a shafinsa na Facebook wadda a ciki ya yi barazanar zai kashe wadansu ’yan sanda da iyalansu, ya kuma zargi Rundunar ’Yan Sanda ta Los Angeles da korarsa daga aiki ba bisa ka'ida ba a shekarar 2008.
Ranar Talata farautar da ake yi ta tsohon dan sandan ta kawo karshe bayan kwanaki shida.

Bam ya tashi a Jihar Bornon Najeriya

Babban Hafsan Dakarun Tsaron Najeriya, Admiral Ola Ibrahim


Wani bam ya tashi da yammacin jiya lokacin da wadansu maharan suka tunkari motocin sunturi na jami'an tsaro na Rudundunar Hadin Gwiwa ta JTF a kasuwar Gambaru, daura da babbar hanyar zuwa Gamboru-Ngala a Jihar Borno da ke arewacin Najeriya.
A wata sanarwa da ta fitar, rundunar ta JTF ta tabbatar da faruwar al'amarin, tana mai cewa sanadiyar fashewar bam din wuta ta watsu ta kona gidaje da shagunan da ke kewaye da wajen.
A sanarwar mai dauke da sa hannun kakakinta, Laftanar Kanar Sagir Musa, rundunar ta ce mutane biyu—wadanda ake zargin maharan ne—da wani soja daya sun rasa rayukansu.
Ta kuma ce bam din ya yi kaca-kaca da wata motar rundunar ta JTF, ko da yake babu wani farar hula da abin ya shafa.

Friday, 15 February 2013

An zargi shirin rediyo da jaza kasan ma’aikatan allurar Foliyo

 


A ranar Talatar da ta gabata ne aka gurfanar da tsohon Darakata Janar din Hukumar Tace Fiian-finai ta Jihar Kano,  Malam Rabo Abdulkarim da ‘yan jarida da ke aiki da gidan rediyon Wazobiya wadanda suka hada da Yakubu Musa Fagge da Mubarak Sani Muhammad
, a gaban wata kotun majistare mai lamba 17 da ke unguwar Gyadi-gyadi cikin Jihar Kano bisa zarginsu da laifin hadin baki bisa tunzura jam’a  su kyamaci allurar rigakafin shan inna tare da cin zarafin Hakimin Tarauni dan goribar Kano a cikin shirin gidan rediyon wazobiya na ‘Sandar Girma.’
Tunda farko mai gabatar da kara Sajan Sadik Na’abba  a cikin takardar karar da ya karanta a gaban kotun ya bayyana cewa,. “Kai Malam Rabo Abdulkarim wanda ke zaune a gida mai lamba 155 a kan titin Maiduguri a karamar Hukumar Tarauni ka bijire wa ma’aikatan allurar rigakafin shan inna inda ka nuna ba za su yi wa ‘yayanka ba. Hakan ya jawo Hakimin Taruni da sauran shugabnnin da ke kula da aikin allurar suka je gidanka don sanin dalilinka na kyamar allurar. Amma sai aka samu ka hada baki da wadansu ‘yan jarida da ke aiki a gidan rediyon Wazobiya inda suka gabatar da wani shiri na ‘ Sandar Girma’  don tunzura jama’a su kyamaci allurar Foliyo din tare da cin mutuncin Hakimin Tarauni. Har ila yau kuma hakan shi ya yi sanadiyar da aka kai wani hari har aka kashe wasu ma’aikatan foliyo a kanan hukumomin Tarauni da kuma Nassarawa wanda hakan laifi ne da ya saba wa sashe na 97 da 85 da 399 da 392 da 393 na kundin laifuka na Finalkod (pinal code).
Sai dai dukkanin wadanda ake zargin sun musanta laifin da ake zargin su da shi.
Mai shari’a Bello Ibrahim ya dage sauraren shari’ar zuwa ranar 14 ga wannan watan don ci gaba da sauraran shari’ar, tare da bayar da umarnin ci gaba da tsare wadanda ake zargi har zuwa ranar da za a ci gaba da saurarn shari’ar.
Rundunar  ‘yan sandan Jihar Kano dai ta kama ‘yan jarida wadanda ke aiki da gidan rediyon Wazobiya FM da kuma tsohon Darakta Janar na Hukumar tace Fina-finai ta Jihar Kano, Malam Rabo Abdulkarim ne inda take bincikensu game da wani shiri da gidan rediyon ya watsa a makon da ya gabata a game da cutar foliyo.
‘Yan jaridar da ‘yan sandan suka kame sun hada da Shugaban sashin shirye-shirye na gidan rediyon Wazobiya Muhammad Sulaimanu Gama da kuma maishiryin wani shiri mai suna ‘’Sandar girma’’ Yakubu Musa Fagge da kuma  mai dauko rahoto, Mubarak Muhammad Sani.
Shugaban gidan rediyon na Wazobiya Malam Sanusi Bello Kankarofi ya bayyana wa Aminiya cewa, a ranar Lahadin da ta gabata ne rundunar  ‘yan sandan ta gayyaci ma’aikatansu guda uku  don bincike.  “Tun daga wancan rana kuma aka tsare ma’aikatan namu ba tare da wani dalili ba. Mun nemi su sanar da mu wane shiri ne muka sanya a rediyo wanda har ya jawo aka aiwatar da hari a kan ‘yan sandan da ke yi wa ma’aikatan alluar rigakafin cutar shan inna rakiya, amam sun kasa ba mu amsa. Mu muna ganin ana so a yi amfani da wannan dama ne a wulakanta ‘yan jarida saboda wani dalili na siyasa.” Inji shi.
Sai dai a hirar da ya yi da manema labarai, Kwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano Alhaji Ibrahim K. Idris ya musanta wannan zargi, inda ya ce, “Babu shakka mun kama wadannan mutane, sai dai ba mu kama su a matsayinsu na ‘yan jarida ba, sai don gudanar da wani bincike da muke yi. Da zarar mun kammala bincikenmu za mu sanar da jama’a halin da ake ciki.” Inji shi.
Aminiya ta samu damar tattaunawa da Malam Rabo Abdulkarim a lokacin da yake tsare, inda ya bayyana wannan kame a matsayin cin zarafin bil’Adama, “Tun da dai mun san a kan gaskiya muke to muna yi wa Allah godiya. Babban fatanmu shi ne game da wannan ma’amala ta allurar rigakafin shan inna a daina tursasa talakawa a kai, ba wai a kan wannan kawai ba, dukkanin wadansu abubuwa da aka kawo komai kyawunsu bai kamata a turasasa jama’a a kai ba. Abin da ya kamata a yi shi ne a yi kokarin ilimantar da jam’ar har su gane alfanun da ke cikin lamarin. Yadda mutne za su rika yin mua’amala kowace iri ce bisa ra’aiyin kansu da kuma bisa ilimantar da su da aka yi.”
Shi ma a nasa bangaren, mai gabatar da shirin na ‘Sandar Girma’  Yakubu Musa Fagge ya bayyana cewa babu wani abu na hadin baki tsakanin gidan rediyonsu da Malam Rabo wajen aikewa da ma’aikacinsu, haka kuma ba shirinsa na Sanda ne ya jawo aka kai hari kan ma’aikatan foliyo ba. “Gaba daya dai laifin da ake tuhumarmu da shi, shi ne mun hada baki da Malam Rabo wajen aika wakilinmu don ya dauki rahoton  takaddamar da za ta faru tsakaninsa da masu allurar shan inna. Hakan ya sa na ba wa ‘yan sandan hujjoji guda uku wadanda suka karyata hakan, sai dai sun ce har yanzu suna nan suna gudanar da bincike. Haka kuma shirinmu na Sanda ba shi ne ya jawo aka kai hari a kan ma’aikatan foliyo ba.” Inji Yakubu.
Aminiya ta samu zantawa da Shugaban sashin shirye-shirye na gidan Rediyon Wazobiya Muhamamd Sulaiman Gama jim kadan bayan an bayar da belinsa, ya bayyana wa Aminiya cewa duk da cewa ba a gaya musu laifin nasu kai tsaye ba, amma an sanar da su cewa shirinsu na Sanda shi ne ya tunzura jama’a kyamatar allurar rigakafi, haka kuma shirin ne ya jawo ‘yan bindiga suka kai hari a kan ma’aikatan foliyo. “Rigimar ta fara ne bayan an doki ma’aikacinmu a lokacin da ya dauki rahoto a kan rigimar rigakafin allurar  tsakanin Malam Rabo da tawagar masu tabbatar da cewa an yi allurar har aka kwace masa kayan aikinsa, hakan ya sanya mai gabatar da shirin Sanda ya tabo waccan magana a cikin shirinsa wacce kuma ba ta yi musu dadi ba. Haka kuma sai ga shi washegri an kai hari kan masu allurar rigakafin har aka kashe mutum tara a cikinsu. Wannan ne ya sa aka ce ana tuhumar ma’aikatanmu.” Inji shi.
Binciken Aminiya ya gano cewa ‘yan sanda suna kokarin hada alaka tsakanin shirin da gidan rediyon Wazobiya ya gabatar da kuma harin da aka kai washegari kan ma’aikatan foliyo a jihar, inda suke zargin shirin na sanda da hura wuta tare da tunzura jama’a kyamar allurar polio.
Idan za a iya tunawa a ranar Talata biyar ga watan Fabreru  dan jarida da ke aiki da gidan rediyon Wazobiya ya sha da kyar sakamakon dukan da wadansu matasa suka yi masa a daidia lokacin da yake gudanar da aikinsa.
Kamar yadda dan jaridar da ya sha dukan mai suna Mubarak Muhammad Sani ya bayyana wa Aminiya, ya ce a daidai lokacin da yake hira da tsohon Shugaban Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano, Malam Rabo Abdulkarim a gidansa a kan wani lamari daban, sai ga tawagar da ke lura da allurar rigakafin sun shigo gidan wadanda suke son ganin Malam Rabo a kan wata magana ta daban. “Lokacin da muke tattunawa da Malam Rabo sai tawagar masu allurar rigakafin, da ta kunshi Shugaban Riko na karamar Hukumar Tarauni da Hakimin Tarauni da kuma wadansu ‘yan bangar siyasa,da wanda na ke zaton ‘yan jam’iyyar PDP ne, domin dukkaninsu suna sanye da jajayen huluna, sai suka shigo gidan inda suka nemi mu dakatar da abin da muke yi har sai sun gama abin da ya kawo su gidan. A lokacin da na fuskanci tirka-tirka da mujadala ta kaure a tsakaninsu sai na fara daukar labarin. Yayin da suka fuskanci abin da nake yi  sai Hakimi ya ba wa matasan nan umarni da  su fitar da ni waje tare da duka na.”
dan jaridar ya kara da cewa, “Na yi kokari  wajen fahimtar da su abin da ya faru amma suka ki saurara ta, inda suka yi kwallo da ni zuwa waje, suka yi min duka, ta hanyar hada hannayensu bibbyu suka rika dukana a fuskata da gefen kunnuwana. Saboda tsananin duka wallahi kasa gane abin da yake faruwa na yi. Sai na rika jin wani dum a kaina.”
Malam Mubarak wanda yake kwance a gida yake jinyar raunikan da ya samu a lokacin wanann waki’a, ya bayyana cewa, tawagar ta kwace wayarsa da rediyon daukar maganarsa  tafi da su, sai da shugabanninsa suka sanya baki sannan aka dawo masa  da kayayyakinsa.
A lokacin da Aminiya ta tuntubi mai taimaka wa Gwamnan Kano a kan harkokin watsa labarai, Ja’afar Ja’afar ya musanta faruwar wannan lamari, inda ya ce babu wani mutum mai halkali da zai sa a doki wani, ballanatan kuma bababn mutum kamar Hakimi. “Wanann magana babu gaskiya a cikinta. Ta yaya ma babbn mutum kamar Hakimi zai sa a doki dan jarida. Ban da ma haka yaya za a yi a tabbatar da cewa mutanen da suka yi dukan ‘yan PDP ne don kawai sun sanya jar hula? Kowa ma zai iya sanya jar hula ya badda kama a matsayin dan jam’iyyar PDP.” inji Ja’afar.
A washegarin ranar  Laraba ne a cikin shirin Sandar Girma gidan rediyon Wazobiya ya bayar da rahoto game da dukan kawo wuka da aka yi wa wakilinsu a lokacin da yake gudanar da aikinsa na daukar rahoto a kan tirka-tirkar da ke faruwa game da allurar rigakafin cutar shan inna.  An ce dai wanann shiri ne ya ja musu jangwam inda ake zarginsu da laifin tunzura jama’a bisa kyamar allurar rigakafin.

Kotu ta bukaci a tsare Shugaba Al Bashir

Omar Al Bashi na Sudan

Kotun manyan laifuka ta duniya ta bukaci Kasashen Chadi da Libya da su tsare Shugaba Omar al Bashir na Sudan, sannan a tusa keyarsa domin ya fuskanci shari'a, idan har ya ziyarci Kasashen biyu a karshen mako
Wannan umarni shine yunkurin Kotun dake Hague na baya bayan nan na ganin cewa an tsare shugaban
Ana dai zargin sa da shirya kisan kare dangi da kuma aikata laifukan yaki a yankin Darfur na Sudan
Kasashen Chadi da Kenya da wasu kasashen Afirka da dama sun karbi bakwancin Mr Bashir, duk da cewa dukkanin su sun amince da kotun manyan laifukan

Wani makeken dutse zai wuce kusa da duniya

 Makeken dutse


Wani makeken dutse mai girman kusan filin kwallo zai wuce ta kusa kusa da duniya a cikin yan sa'o'i masu zuwa.
Dutsen -- mai fadin murabba'in mita 45, ana sa ran zai kusanci duniya da kusan nisan kilomita dubu 28 -- kurkusa fiye da tauraran dan adam da kuma masu nazartar yanayi.
Masana ilmin kimiya sun ce babu hadarin cewar dutsen na Asteroid zai fado kan doron duniya, kuma ba shi da wata nasaba kwata kwata da mulmulen dutsen Meteor na Rasha .
Wata masaniyar kimiya a Jami'ar koyo daga gida a Milton Keynes, Farfesa Monica Grady ta ce lamuran biyu ba su da nasaba da juna.

Oscar Pistorius zai fuskanci shari'a

Kwararru za su gana game da naman doki

 

A ranar Juma'a ne kwararru kan harkar kula da ingancin abinci a nahiyar Turai za su gudanar da taro a Brussels don tattaunawa kan badakalar nan ta sayar da naman doki a matsayin naman shanu.
Hakan na zuwa ne yayin da 'yan sanda a Burtaniya suka kama mutane uku da ake zargi da hannu da sayar da naman doki a matsayin naman shanu.
Tun da farko hukumomin kasar Faransa sun soke lasisin wani kamfanin kasar da ake zargi da sayar da fiye da tan dari bakwai na naman doki a matsayin naman shanu.
Sai dai Kamfanin mai suna, Spanghero, ya musanta zargin.
Wadansu manyan shaguna a kasar Jamus sun fara janye naman shanun da ake sayarwa a shagunansu.
 


A ranar Juma'a za a gurfanar da zakaran tseren nakasassu na Afrika ta Kudu, Oscar Pistorius, a gaban kuliya saboda zargin da ake yi masa na kashe budurwarsa a gidansa da ke Pretoria.
An harbi Reeva Steenkamp sau hudu a kanta da wadansu sassan jikinta ranar Alhamis.

Ba ta dade ba ta mutu.
'Yan sanda sun ce sun samu wata karamar bindiga a wajen da ta mutu.
Tun da farko 'yan sanda sun yi wa Mista Pistorius tambayoyi.
Daga bisani an kai shi wani asibiti domin gwada jininsa.

Thursday, 14 February 2013

Iyalan masu rigakafin polio da aka kashe sun samu tallafi

 Wata jami'ar rigakafin  shan inna

Iyalan ma'aikatan rigakafin shan inna ko polio da aka kashe a jihar Kano a makon jiya, sun samu tallafin naira miliyan daya kowannensu.
Gwamnatin jihar ce ta basu naira dubu dari biyar, yayin da shahararren mai kudin nan na Najeriya, kuma dan asalin jihar Aliko Dangote, kuma ya basu tallafin naira dubu 500.
Kimanin mata tara ne suka mutu a lokacin da wasu 'yan bidiga suka bude musu wuta a ranar Juma'ar data gabata.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ake sa ran ministan lafiya na kasar zai kai ziyara jihar Kano game da harin.

An harbe wani matashi a zanga zangar Bahrain

 Zanga Zanga a Bahrain

An harbe wani yaro har lahira a kasar Bahrain, a lokacin wata zanga-zanga domin cika shekaru biyu da juyin-juya halin da baiyi nasara. Wasu mutenen da dama sun samu raunuka lokacin da masu zanga-zangar adawa da gwamnati suka kafa shingaye akan hanya sannan suka yi arangama da jami'an tsaro. Gwamnatin Bahrain ta tabbatar da mutuwar wani yaro dan shekaru sha shida amma tace ba a san dalilan mutuwar ta sa ba. Wani mai fafutuka na 'yan adawa Radi Al-Musawi, ya shaida wa sashin Larabci kan yadda lamarin ya faru