Monday, 11 March 2013

Burkutu ta kashe mutane da dama a Libya

Libya

Mutane sama da hamsin ne ake cewa sun mutu daga cikin daruruwa da aka kwantar a asibitoci a duk fadin Turabulus, babban birnin kasar Libya, sakamakon shan gurbatacciyar giyar gargajiya wato burkutu.
Ma'aikatar lafiya ta Libyar ta yi shelar cewa an shiga wani yanayi na ta-baci, a asibitocin kasar.
Tun daga ranar Asabar aka fara samun mace macen, kuma adadin ya ci gaba da karuwa.

An gayyato Kamfanonin Dubai zuwa Kano

 Gwamnan Kano Rabiu Kwankwaso
Gwamnatin jihar Kano ta ce ta cinma wasu shirye shirye da wasu kamfanoni a Dubai, wadanda za su je Kanon su saka jari a harkar da ta shafi sufurin jirgin kasa da zai rika zirga zirga a cikin birnin Kano.
Baya ga wannan gwamnatin Kanon na tattaunawa da wasu kamfanonin Dubai domin su zuba jari a bangaren hasken wutar lantarki da kuma kafa jami'a mai zaman kanta.
Gwamna Rabi'u Kwankwaso ya shaidawa  cewa a watan gobe su ke sa ran daddalewa kan wadannan batutuwan da mutanen da suka gayyata zuwa Kano.
Jahar Kano dai ta yi fama da matsalolin hare haren 'yan bindiga abinda ya kawo cikas ga harkokin kasuwanci

Babu shaidar kisan 'yan Setraco - Najeriya

 Kanal Sambo Dasuki

Gwamnatin Najeriya ta ce ba a tabbatar da ikirarin kisan 'yan kasashen waje bakwai, ma'aikatan Setraco da aka kama a jihar Bauchi ba.
Saboda haka za ta yi iya bakin kokarinta wajen ceto su, da kuma tabbatar da tsaron lafiyarsu.
Ministan harkokin wajen kasar, Abba Moro ne ya bayyana hakan.
Inda ya kara da cewa, abin takaici ne yadda al'amarin ya kai ga haka.
Ya ce "Duk da cewa kasashen da ma'aikatan suka fito sun yi amanna an kashe 'yan kasashensu, babu hujjar dake tabbatar da hakan, kuma muna fatan suna raye."
Kungiyar masu fafutukar Islama ta Ansarul Muslimina fi Biladis Sudan ce, ta kame mutanen a watan jiya, a wurin da suke aikin gine-gine a arewacin Najeriya.
Kuma tuni kasashen Birtaniya da Italiya da Girka su ka ce, sun yi amanna an kashe mutanen bakwai a Najeriya, kamar yadda kungiyar Ansaru ta bayyana a wani faifan bidiyon da ta sanya a shafin intanet.
A cewar kungiyar, ta kashe 'yan kasashen Birtaniya da Italiya da Girka da Lebanon da ta yi garkuwa da su ne, saboda yunkurin da dakarun Birtaniya da na Najeriya suka yi na ceto su.
Amma Italiya ta ce babu kamshin gaskiya a wannan batu.
Sakataren Harkokin Wajen Birtaniya, William Hague, ya yi tur da al'amarin.

Wani dansanda ya kashe kansa a india

 
Tahir gidan yarin da aka sami gawar Ram wanda ake zargi da fyade
Babban wanda ake zargi da yin fyaden taron dangi a birnin Delhi na India an same shi a mace a dakinsa na gidan yari.
Ram Singh, na daya daga cikin samari biyar da ake zargi da fyade da kuma kisan wata yarinya 'yar makaranta a watan Disambar bara.
Lauyan da yake kare babban wanda ake tuhumar da fyaden ya ce 'yan sanda sun kirashi sun shaida masa cewa wanda yake karewa ya kashe kansa.
Ram Singh, shine matukin motar kirar Bus din da aka yiwa 'yar makarantar kazamin fyaden.
Mutuwar Mr Singh za ta jawowa Hukumomi abin fada wanda tuni suna samun matsin lamba kan shari'ar.

Saturday, 9 March 2013

An sake kwantar da Nelson Mandela a asibiti

Nelson Mandela
An sake kwantar da Tsohon Shugaban Afirka ta Kudu Nelson Mandela asibiti saboda abinda jami'ai su ka ce sake duba lafiyar sa , kamar yadda aka tsara
Mai magana da yawun Shugaba Jacob Zuma yace likitoci na duba lafiyar Mandelan game da wa ta laurar da yai fama da ita
Mr Mandela wanda yake da shekaru casa'in da hudu a duniya, ya shafe kusan makonni uku a watan Disambar bara wance a gadon asibiti, bayan da yai fama da cutar huhu.
Ana dai girmama Mandela sosai a nahiyar Afirka

Uhuru Kenyata ya ce zai yi aiki tare da Raila Odinga

 Uhuru Kenyatta, zababben Shugaban Kenya

Sabon Zababban Shugaban Kasar Kenya Uhuru Kenyatta ya dau alkawarin aiki tare da wanda ya kayar, kuma abokin hamayyarsa Raila Odinga, da kuma yiwa dukkanin 'yan Kasar Kenya aiki a kalamansa ba kuma tare da tsoro ko nuna alfarma ba
An bayyana Mr Kenyatta wanda ya lashe zaben na ranar litinin da 'yar karamar , inda ya samu kashi hamsin da digo bakwai cikin dari na kuri'un da aka kada
Amma Mr Odingan yace zai kalubalanci sakamakon zaben a kotu.
Ya kuma yi gargadin cewar duk wani tashin hankali ka iya dagula kasar
Mr Kenyatta dai na fuskantar shari'ah a kotun hukunta manyan laifuka ta duniya dake Hague, bayan da aka zarge shi da hannu a tashin hankalin da ya biyo bayan zaben shekarar 2007

An kashe 'yan ƙasashen waje 7 a Najeriya

 

Wata ƙungiyar masu gwagwarmaya da makamai a arewacin Najeriya mai suna Ansarul muslimina fi biladi sudan tace ta kashe 'yan ƙasashen waje bakwai da ta sace a watan da ya gabata.
Ƙungiyar ta Ansaru tace ta ɗauki wannan matakin ne saboda dakarun Najeriya da na Faransan sun kashe musulmi a wani farmakin da suka kai na ƙoƙarin su na 'yanto waɗanda aka yi garkuwar da su.
Mutanen da aka yi garkuwar da su dai ma'aikata ne na wani kamfanin gine gine mallakar 'yan Lebanon
Uku daga cikin mutanen dai 'yan Labanon ne, sauran hudun kuwa sun fito ne daga ƙasashen Burtaniya, da Girka, da Italiya, da kuma Philippines.
Ana dai tunanin cewa ƙungiyar ta Ansaru, ɓangare ne na ƙungiyar Boko Haram wacce aka yi imanin cewar ita ke riƙe da iyalan Faransawan nan da aka sace a Kamaru.

Friday, 8 March 2013

Yan sandan da ake zargin kisan dan Taxi na kotu

A kasar Afrika ta kudu wasu 'yan sandan kasar su 9 sun gurfana gaban Kotu inda aka yi zaman sauraren kara ta neman belinsu dangane da mutuwar wani direban Taxi dan kasar Mozambique.
An sanya wa Mido Macia ne ankwa aka daure shi jikin motar 'yan sanda aka rinka jan sa a kan titunan Daveyton dake kusa da Johannesburg.
Dukkan 'yan sandan 9 dai sun ce ba su da laifi ga cajin da aka yi musu na kisan kai.
Hoton video na abinda ya faru da wasu suka dauka da wayar salula wanda aka nuna a gidan talabijin na kasar ya tunzura mutane a sassa daban-daban na kasar.

An bawa Malamai bindiga a Amurka

 Jihar South Dakota dake kasar Amurka ta zartar da wata doka wadda ta amince wa makarantun yankin baiwa Malaman makaranta da sauran ma'aikatan makarantun bindigogi don su rinka bayar da kariya ga dalibansu.
Ita ce Jiha ta farko da ta amince da haka tun bayan wani kisan gilla da aka yi a Newtown cikin watan Disambar bara inda aka kashe yaran makarantar ashirin da malamai shida.
Uta da wasu larduna a Texas dama sun rigaya sun amince wa malamai su rika rike bindigogi.
Gwamnan jihar South Dakota Dennis Daugaard ya ce a Jihohi na karkara kamar na su, ba kasafai a kan samu jami'an tsaro a kusa ba.

Ana jana'izar Hugo Chavez a Venezuela

 An fara jana'izar Hugo Chavez

An fara jana'izar shugaban Venezuela Hugo Chavez a Caracas babban birnin kasar.
Kimanin shugabannin kasashen duniya 30 ne ke halartar bikin a makarantar sojoji inda dandazon jama'a suka taru a waje.

Nan gaba, za a rantsar da mataimakin shugaban kasa Nicolas Maduro a matsayin shugaban riko. Wajibi ne ya sanya ranar gudanar da zabe cikin kwaniki 30.
Hugo Chavez, wanda ya shugabanci Venezuela tsawon shekaru 14, ya mutu ranar Talata yana da shekaru 58 bayan da ya dade yana fama da cutar daji.
Mataimakin shugaban kasa Maduro ne ya fara bude bikin da sanya takobi kan gawar Mr Chavez - takobin na Simon Bolivar ne - wanda ya jagoranci neman 'yancin kan kasar a karni na 19.
Daga nan ne shugabanni suka fara yin layi domin girmamawa ga gawar ta sa.
Rukunin farko shi ne na shugabannin Latin Amurka - wadanda suka kunshi Raul Castro na Cuba, Sebastian Pinera na Chile da Rafael Correa na Ecuador.
Wani rukunin kuma shi ne na kawayen Mr Chavez daga wajen yankin, shugaban Iran President Mahmoud Ahmadinejad da Alexander Lukashenko na Belarus.
An kuma karanto sakon shugaban kasar Syria Bashar al-Assad.

'Yan sanda sun kama Carlos Tevez

 Carlos Tevez

BBC ta fahimci cewa 'yan sanda sun kama dan wasan Manchester City Carlos Tevez a garin Cheshire kan zargin tuka mota duk da cewa an kwace lasisinsa na tuki.
Tevez, mai shekaru 29, an tsare shi ne ranar Alhamis da misalin karfe 5:10 agogon GMT a kan titin A538 a Macclesfield.

Amma 'yan sanda sun bayar da belinsa.
An dakatar da dan wasan na Argentina daga tuki tsawon watanni shida a watan Janairu bayan da yaki amsa wasikar da 'yan sanda suka aika masa kan gudu a mota fiye da kima.
Manchester City ta ce ba za ta yi magana a kan batun ba.
Mai magana da yawun 'yan sandan Cheshire ya ce: "Jiya 'yan sanda sun kama wani mutum mai shekaru 29 daga Alderley Edge".
"An kama mutumin ne kan zargin tuka mota duk da cewa an kwace lasisinsa sai dai tuni aka riga aka bayar da belinsa."

Jonathan ya kalubalanci dattawan Borno

 Goodluck Jonathan

A ci gaba da ziyarar da ya ke yi a jihohin Borno da Yobe wadanda su ka fi fama da rikicin da ake yi tare da kungiyar nan ta jama'atu ahlissunnah lid da'awti wal jihad da wasu ke kira Boko Haram, Shugaban Najeriya Dr Goodluck Jonathan a yau ya gana da shugabanni da dattawa da kuma 'yan siyasa na Jihar ta Borno.
Wasu dattawan jahar Bornon dai sun bukaci Shugaban ya bada iznin janye sojoji daga jahar, inda su kai zargin cewa sojojin su na gallazawa jama'ar jahar.

To sai dai a martanin da ya mayar Shugaba Goodluck Jonathan ya kalubalanci dattawan Bornon da har sai sun bashi tabbacin cewar ba za a cigaba da samun asarar rayuka ba idan aka janye sojojin, kafin ya amince da wannan bukata ta su.
Shugaban ya ce gwamnati bata jin dadin irin kudaden da take kashewa akan maganar tsaro a yankin, kudaden da Shugaban ya ce za a iya karkatar da su wajen wasu fannoni na ayyukan raya kasa.
Amma ya ce idan har dattawan zasu sanya hannu kan wata yarjejeniya da shi na cewa idan an janye sojojin ba za a ci gaba da samun asarar rayuka ba, ya ce to a shirye yake ya bada iznin janye sojojin
Haka kuma ya sake jaddada cewa babu maganar yin afuwa ga 'yan kungiyar Boko Haram har sai 'yan kungiyar sun fito sun bayyana aniyarsu ta amincewa da hakan.

Ferguson: Rooney na nan daram a United

 Wayne Rooney da Ferguson

Kocin Manchester United Sir Alex Ferguson ya yi alkawarin cewa Wayne Rooney zai ci gaba da zama a kulob din har kakar wasanni mai zuwa.
Dan wasan mai shekaru 27, ba a fara wasan da United ta yi da Real Madrid a zagaye na biyu na gasar cin kofin zakarun Turai da shi ba, inda Ferguson ya fara amfani da Danny Welbeck.

Wannan ya haifar da rahotonni da dama a jaridun Ingila cewa United za ta sayar da dan wasan a karshen kakar bana.
"Zai kasance tare da mu badi, " a cewar Ferguson. "Na tabbatar muku da wannan."
Ferguson yana magana ne a karon farko tun bayan da aka baiwa Nani jan kati cikin yanayi mai rudani a wasan da United ta sha kashi da 3-2 bayan wasa gida da waje a hannun Real Madrid.
"Wannan ne karo na uku da aka fitar da mu saboda matakin da alkalin wasa ya dauka, abu ne mai matukar wahala amincewa da wannan hukunci," a cewarsa.
Rooney, wanda rahotonni suka ce yana karbar fan 250,000 a kowanne mako a matsayin albashi, ana alakanta shi da komawa kulob daban-daban, cikin harda Paris Saint-Germain.

Mahakar Uranium ta Imuraren za ta soma aiki a 2015

 Mahamadou Issoufou

A Jamhuriyar Nijar kamfanin AREVA mai hakar Uranium a kasar ya ce a tsakiyar shekara ta 2015 ne zai fara aikin hakar uranium din yankin Imuraren.
Mataimakin Darekta Janar na kamfanin na AREVA Mista Olivier Wantz ne ya tabbatar da haka jiya a birnin Yamai.
Yankin na Imuraren dai na iya samar da tan dubu biyar kowacce shekara har tsawon shekaru arba'in
Idan aka soma aikin, Nijar za ta kasance kasa ta farko mai arzikin Uranium a nahiyar Afirka.

Tuesday, 5 March 2013

Buhari ya soki tsarin zabe a Najeriya

 

Dan takarar shugabancin Najeriya karkashin inuwar jam'iyyar adawa ta CPC a zaben shekara ta 2011, Janar Muhammadu Buhari ya ce, har yanzu ba a je ko'ina ba dangane da gyara ga tsarin zaben Najeriya.
Yayin wata lacca da ya gabatar a taron da 'yan Najeriya mazauna kasashen waje suka shirya da hadin gwiwar 'yar majalisar dokokin Birtaniya, Diane Abott, Buhari ya kuma ce, matsalar Najeriya ita ce, cin hanci da rashawa da kuma lalacewar sha'anin mulki.
Janar Buhari ya ce yanzu babban karan tsaye shine shirya zabe cikin gaskiya da adalci.
Ya ce ko da an murde zabe anje kotu, an gudu ne kawai ba'a tsira ba.
"Ya kamata a Hukumar zabe ta Najeriya ta tabbatar an gudanar da zabe a kan adalci kuma bisa ka'ida." in ji Buhari.
Tsohon dan takarar shugaban kasar ya ce sake fasalta Najeriya ba zai kawo karshen matsalolin da ake fuskanta ba a kasar.
Janar Buhari ya ce shugabanci na gari ne kawai zai iya sanya kasar kan turbar ci gaba.
Laccar da aka yi a majalisar dokokin Birtaniya ta samu halartar 'yan Najeriya da dama dake zaune a Birtaniya.

Duba yadda za'a kare ma'ikatan rigakafi a duniya



A yau ne za a fara wani taro na kwanaki biyu tsakanin wasu malaman addinin Musulunci da jami'an hukumar lafiya ta duniya, WHO, a birnin Alkahira na kasar Masar.
Taron zai lalubo hanyoyin kawo karshen hare-haren da ake kaiwa masu digon maganin rigakafin cutar polio a wasu kasashe.
Za a gudanar da taron ne a asirce inda za kuma a tattauna rawar da al'ummar musulmi za su taka dan tabbatar da cewa an kare dukkan yara daga kamuwa da cutukan shan inna mai nakasa yara da kyanda da ma sauran cututtuka.
Kimanin ma'aikatan riga-kafin shan inna 20 ne aka kashe a Pakistan da Najeriya cikin watanni uku da suka gabata
Hakan dai wani babban koma baya ne ga fafutukar kawo karshen cutar polio a duniya.
Kasashen Najeriya da Pakistan da Afganistan ne kawai har yanzu suka rage a duniya suna fama da cutar ta polio.
A arewacin Najeriya musamman, mutane na ci gaba da kyamar allurar rigakafin cutar ta Polio.

Shugaban kasar Venezuela Hugo Chavez ya rasu


Mataimakin shugaban kasar Venezuela ya bayyana rasuwar shugaban kasar Hugo Chavez bayan ya yi fama da wata doguwar rashin lafiya.
Mr Chavez dai bai fito a bainar jama'a ba tun bayan da ya dawo daga Cuba inda aka yi mishin maganin ciwon sankara.
Mataimakin shugaban kasar Nicolas Maduro ya bayyana rasuwar shugaban kasar ne cikin kaduwa.
Shugaban kasar mai shekarun haihuwa 58 ya yi fama da matsalar nunfashi ne kafin ya rasu.

Real Madrid ta fitar da Man United

real madrid da manchester united

Manchester United ta sha kashi a hannun Real Madrid a Old Trafford da ci 2-1 da hakan ya sa ta fice daga gasar Zakarun Turai da ci 3-2 gida da waje.
Manchester United ta ci kwallonta ne bayan da Sergio Ramos na Real Madrid ya ci kansu a minti na 48 bayan an dawo daga hutun rabin lokaci.

Luka Modric ya ramawa Real Madrid a miniti na 66, sannan kuma minti uku tsakani Cristiano Ronaldo ya kara ta biyu.
Jumulla wasa gida da waje Real Madrid 3 Manchester United 2.
Real Madrid ta shiga zagayen wasan gab da na kusa da karshe, United kuwa ta yi waje daga gasar Zakarun Turai.
A daya wasan na Kofin Zakarun Turan Borussia Dortmund ta Jamus a gidanta ta casa Shakhtar Donetsk ta Ukraine 3-0.
Felipe Santana ne ya fara jefa kwallo a ragar bakin a minti na 31 sai Goetze ya kara ta biyu bayan minti 6.
A minti na 59 ne kuma Blaszczykowski ya ci kwallo ta uku.
A karawar kungiyoyin ta farko a Ukraine sun tashi 2-2, da sakamakon na yanzu Borussia Dortmund na da kwallaye 5 yayin da Shakhtar Donetsk ke da 2.
Borussia Dortmund ta shiga jerin kungiyoyi 8 da za su fafata a wasan gab da na kusa da karshe.

Man United za ta yi cinikin Schlupp

jerry schlupp

Kungiyar Leicester City na gab da kammala tattaunawa da Manchester United kan sayar da matashin dan wasanta Jeffrey Schlupp
Schlupp mai shekara 20 ya kai sama da wata daya a Old Trafford ana jarraba shi kuma ya buga wasan 'yan kasa da shekara 21 tsakanin United da Liverpool da kuma West Ham a makon da ya wuce.
Schlupp wanda aka haifa a Jamus ya ke bugawa kasarsa Ghana wasa yana wasa ne a gaba amma kuma ya yi wa Leicester wasa a baya ma.
Tsohon kociyan Leicester Sven-Goran Eriksson ya ce bai sani ba ko matashin dan wasan ya kai munzalin tafiya Manchester United wanda ya ce babban ci gaba ne ga dan wasan amma kuma babban rashi ga Leicester.

Ya kamata a yi wa Boko Haram afuwa

 Sarkin Musulmin Najeriya Alhaji Abubakar Sa'ad na uku

Sarkin Musulmin Najeriya Alhaji Abubakar Sa'ad na uku, ya yi kiran da a baiwa 'yan kungiyar Jama'atu Ahlil Sunnah Lid da'awati Wal Jihad da aka fi sani da Boko Haram afuwa.
Ya bayyana cewa wannan matakin zai taimaka wurin kawo karshen tashe-tashen hankulan da ake fama da su a arewacin kasar.
"Za ta sa matasa da dama su fito daga wurin buyansu domin rungumar shirin, kuma koda mutum daya ne ya fito fili sai a rungume shi domin isa ga sauran."
Kungiyar Boko Haram da sauran 'yan bindiga na tayar da kayar baya a sassan arewacin kasar da dama, lamarin da yayi sanadiyyar mutuwar daruruwan jami'an tsaro da fararen hula.
Abaya dai an yi kokarin tattaunawa tsakanin gwamnati da kungiyar ta Boko Haram, lamarin da ya ci tura. A makon da ya gabata ma kungiyar ta karyata rahotannin da ke cewa ta tsagaita wuta.

Jagoran al'ummar musulmi

Sarkin wanda ke magana a wurin wani babban taro na kungiyar Jama'atul Nasrul Islam a Kaduna, ya bayyana matsalar tsaro a matsayin wata babbar matsala da ya kamata gwamnati ta warware.
Jama'a da dama sun sha yin kiran gwamnati da ta yi musu afuwa domin fara tattaunawa da su, amma hakan bai yiwu ba.
Sai dai Editan sashin Hausa na BBC Mansur Liman, ya ce akwai yiwuwar gwamnatin Najeriya ta duba kalaman Sarkin, kasancewarsa jagoran al'ummar musulmi a kasar.
Taron ya kunshi malaman addinin Islama da kuma Sarakunan gargajiya Musulmai na kasar.
Shugabannin za su mayar da hankali ne bisa matsalolin tsaro da kiwon lafiya da kuma tattalin arzikin da suka addabi kasar musamman ma a arewacinta.

Ana neman sa wa Koriya ta arewa sabon takunkumi

'Yan kwamitin sulhun majalisar dinkin duniya

Amurka ta yi kira a Majalisar dinkin duniya da a sawa Koriya ta Arewa sabbin takunkumi, wadanda a karon farko zasu shafi fannin hada-hadar kudin kasar, akan gwajin makamin nukiliyar da ta yi watan jiya.
Jakadiyar Amurka, a Mjalisar, Susan Rice ta ce Washington na da goyan bayan China na samar da wani daftarin kuduri da za su shafi tura tsabar kudi daga Koriya ta Arewan da kuma abin da ta kira miyagun ayyukan jami'an diplomasiyyar Koriya ta arewan.
Susan Rice ta ce, abin da zan fada shi ne kan kasashen duniya a hade yake akan adawa da shirin makamin nukiliyar Koria ta arewa.
Jakadan kasar China ya ce tilasne a aikewa Koriya ta arewan wata babbar alamar rashin amincewa abin da ta yi.
Tun da farko Koriya ta arewan ta yi gargadin soke yarjejeniyar da ta kawo karshen yakinta da Koria ta Kudu a matsayin wani martani na kakaba mata takunkumi da kuma atisayen sojin da dakarun Amurka keyi da na Koriya ta Kudu.

Za'a ta rufe makarantun allo a sanigal

Senegal za ta rufe makarantun allo

Kungiyoyin kare hakkin bil'adama sun sha yin gargadi game yanayin wasu makarantun allon
Shugaban kasar Senegal, Macky Sall ya ce gwamnatinsa za ta rufe duk makarantun allon da ba su cimma matakan kare lafiyar da suka kamata ba.
Kalaman na sa dai sun zo ne bayan wasu yara tara sun mutu a wata gobarar da ta tashi a wata makarantar allo da ke kusa da babban birnin kasar, Dakar.
Gobarar dai ta tashi ne, a yayin da yara 45 masu shekaru shida zuwa 12 ke barci a daki daya, wanda aka gina da katako kuma aka yi masa rufin kwano a gundumar Medina.
Ana dai tunanin wutar kendir ce ta haddasa gobarar a ranar Lahadin da ta gabata.
Kuma a lokacin da ya kai ziyara inda gobarar ta auku ne, Mr. Sall wanda Musulmi ne, yace daga yanzu duk makarantar allon da ke ci da gumin yara, kuma ba ta tabbatar da kare lafiyarsu to za a rufe ta.
Sannan za a maida yaran gurin iyayensu.

Muhalli mara kyau

kungiyoyin kare hakkin bil'adama sun sha yin gargadi game da wurare marasa kyau da ake ajiye yara a karkashin ilimin tsangaya.
Haka kuma akwai zargin da ake wa wasu malaman makarantar allon da ci da gumin almajirai.
Yawancin yaran da ake kaiwa karatun na tsangaya na kare wa a matsayin almajirai, inda suke yawon bara, suna neman kudi da abinci domin su kaiwa malaman.
Motocin kashe gobara sunyi ta fama kafin su shiga lungun da makarantar take, abin da ya kawo jinkiri wajen kashe gobarar.
Magajin garin Dakar, Khalifa Sall ya bayyana wa wani gidan radiyon kasar cewa, muhalli mara kyau dake cunkoson jama'a da ake da su a wannan sashen na birnin ne yasa masu kashe gobara suka kasa kutsawa domin yin aikinsu kamar yadda ya kamata.

Monday, 4 March 2013

Ferguson : Ba ma tsoron Ronaldo

 alex ferguson

Yayin da ake shrin karawa ta biyu tsakanin Manchester United da Real Madrid a gasar Zakarun Turai ranar Talatar nan kocin United Sir Alex Ferguson ya ce ba za su ji tsoron Ronaldo ba.
Kociyan ya kafe cewa Manchester United ba za ta ji tsoron Cristiano Ronaldo ba a karawar tasu a Old Trafford duk da cewa shi ya ci United din a karawar farko a Bernabeu da suka tashi 1-1.

Ferguson ya ce ''ba abu ne da zai tada mana hankali ba.
Idan muka damu da ta'annatin da zai iya mana to kuwa zamu manta da abin da zamu iya yi.''
Amma kuma duk da karfin halin na Ferguson ya lamunta cewa dan wasan da ya rena a Old Trafford kafin Real Madrid ta saye shi a kan fam miliyan 80 a 2009 zai iya zamar musu babbar barazana ga fatansu na zuwa wasan gab da na kusa da karshe na Zakarun Turan.
Sir Alex ya ce '' to me kake tsammani idan kana wasa da kungiyar da take da Ronaldo a cikinta?
Ba shakka dole ne ka yi tsammanin matsaloli a lokacin wasan amma za mu yi duk abin da zamu iya mu hana hakan.''
A shekara ta 2003 takwaran Cristiano Ronaldon wato Ronaldo na Brazil ya ci Manchester United kwallaye uku rigis a Old Trafford da suka yi waje da United din a wasan gab da na kusa da na karshe na gasar Zakarun Turai a karawarta da Real Madrid din.

Man City ta kara kusantar United

 aston villa da manchester city

Manchester City ta kara rage ratar da ke tsakaninta da Manchester United ta daya a gasar Premier zuwa maki 12.
Manchester City ta na jagba ne a gasar ta Premier da maki 71 a wasanni 28.
Man City ta biyu a tebur ta samu wannan nasara ce bayan da ta yi galaba a kan Aston Villa wadda ke wasa a gida da ci 1-0.
Carlos Tevez ne ya ci kwallon daya tilo ana gab da tafiya hutun rabin lokaci a minti na 45.
Aston Villa ta ci gaba da kasance wa cikin kungiyoyi uku da ke cikin hadarin faduwa daga gasar Premier inda ta ke matsayi na 18 da maki 24 a jerin kungiyoyi 20.

Yara 800 sun kamu da kyanda a jihar Kano

 Yaro mai fama da cutar gyanda

An samu barkewar cutar kyanda a jihar kano dake arewacin Najeriya, abin da ya sa yara fiye da 800 ke yin jinya a asibitoci daban-daban na jihar.
Kwamishinan lafiya na jihar Dr. Abubakar Labaran yusuf ne ya tabbatar wa yan neman labarai hakan.
Amma dai wasu majiyoyin sun ce yara fiye da dubu daya ne suka harbu da cutar.
Dr. Abubakar ya ce barkewar cutar na da nasaba da shigowar zafi, inda ya nemi iyaye su yi ta kai yaransu rigakafi.
Sai dai wasu rahotannin na cewa an samu karancin allurar rigakafin cutar, abin da ya taimaka wajen barkewarta.
Cutar ta barke ne a wasu kananan hukumomi biyar da suka hada da Tarauni da Gwale da Madobbi da Karaye da kuma Kabo.

Congo: Mutane 30 sun mutu a hadarin jirgi

Congo

Jami'ai a jamhuriyar Demokradiyyar Congo sun ce wani jirgin sama ya fadi a birnin Goma a gabashin kasar, inda mutane talatin suka mutu.
Jirgin, wanda ya taso daga garin Lodja dake yankin tsakiyar kasar, mallakar wani kamfanin kasar ne mai suna CAA.
Jamhuriyar Demokradiyyar Congo dai ta kasance daya daga cikin kasashen da basu da ingantacciyar hanyar sufuri ta sama a duniya.

Sai Arsenal ta yi da gaske - Wenger

 Manajan kulob in Arsenal, Arsene Wenger

Arsene Wenger ya ce za ta yi kokarin shiga gasar champions league, duk da cewa za su kara da Manchester City da kuma Liverpool
Manajan kulob din Arsenal, Arsene Wenger yace sai kulob din ya yi da gaske, kafin ya shiga jerin kulob hudu na gasar premier.
Ya bayyana hakan ne bayan kulob din Tottenham ya doke Arsenal da ci biyu da daya.
Arsenal dai na da maki bakwai, a bayan Spurs wanda kulob na uku ne a gasar, yayin da Chelsea kuma ita ce ta hudu kuma tana gaba da Arsenal da maki goma.
"Lallai sai mun yi da gaske, kuma a yanzu kamar wuri ya kure mana, saboda mun rasa wasu maki da bai kamata ace mun rasa su ba. " A cewar Bafaranshen.
Ya kara da cewa "Amma za mu zage damtse, kuma ba za mu karaya ba."
Tun shekarar 1995 kawo yanzu Arsenal ta kasa shan gaban Spurs, haka kuma ta kasa shiga cikin jerin kulob-kulob hudu na gasar premier tun a shekarar 1996, da ta zo ta biyar.
A halin yanzu kulob din na cikin shekara na 15, yana wasa a gasar champions league.

FIFA na neman mai karbar bakunci

 sepp blatter

 Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya FIFA na neman wata kasar da za ta karbi bakuncin gasar cin Kofin Duniya na mata 'yan kasa da shekaru 17.
Hakan ya biyo bayan gazawar da Costa Rica ta yi ne ta kammala aikin ginin filayen wasa a kan lokaci.
A da dai an baiwa Costa Rica damar gudanar da gasar ce wadda za a yi a shekara mai zuwa.
FIFA ta ce an yanke shawarar neman wata kasar ce tare da ita Costa Rican saboda matsalolin da suka taso da za su haddasa jinkiri mai tsawo da ba a yi tsammani ba a aikin.
A watan Satumba ne na 2014 ake saran gudanar da gasar ta kasashe 16.
Hukumar ta FIFA ta ce za ta yi nazarin wadanda za su nemi karbar bakuncin gudanar da gasar kafin kwamitin zartarwarta ya yanke shawara a taronta daga ranar 20 zuwa 21 na watan Maris a Zurich.
Costa Rica ta samu damar karbar bakuncin ne a watan Maris na 2011 inda ta yi galaba a kan Ghana da Turkiyya da kuma Uzbekistan.

Cardinals za su fara taron zaben Fafaroma

 

Masu mukamin Cardinals a cocin Roman Katolika a yau Litinin za su fara wannan taron sirrin wanda za'a kwashe mako daya ana yi domin zabar sabon Fafaroma bayan murabus din din da Fafaroma Benedict ya yi a ranar alhamis din da ta gabata.
Wanda su ka zaban ne zai jagoranci cocin katolika mai sama da mabiya biliyan daya a duniya.
A mako mai zuma ne ake sa ran za'a fara zaben sabon fafaroma, amma ya zuwa yanzu dai ba a sanya ranar kada kuri'ar ba.
Masu mukamin Cardinals daga fadin duniya dai na ci gaba da isa birnin Rome domin zaben sabon Fafaroma da zai jagoranci cocin Roman Katolika a fadin duniya.
Kashi biyu cikin uku na Cardinals din da ake da su a duniya sun riga sun isa birnin na Rome a karshen makon da ya gabata.
Kasar Burtaniya dai ba za ta samu wakilci ba ba saboda murabus din da Cardinal Keith O'Brien ya yi, bayan ya
amince da zargin yin lallata da ake masa.
Archbishop din Westminster da ya yi murabus wato Cardinal Cormac Murphy O'Connor, zai halarci taron share fage, amma bashi da damar yi zabe saboda ya haura shekaru tamanin.
Amma dai yayi zabe a lokacin da aka zabi Pope Benedict a shekara ta 2005.
A yanzu haka dai za'a tsaurara matakai a Vatican musamman ma game da samun bayanai har sai an zabi sabo fafaroma.

An warkar da wata karamar mai cutar HIV a Amurka

 

Wasu masana a Amurka a karon farko sun warkar da wata karamar yarinya da aka haifa da kwayar cutar HIV mai karya garkuwar jiki a jihar Mississippi.
Dr Deborah Persaud, mai nazarin kwayar cututuka ce ta asibitin Jam'iyyar Baltimore ta bayana irin nasarar da suka samu a wani babban taron nazarin manyan cututuka da aka gudanar a Atlanta.
A yanzu haka dai yarinyar tana da shekaru biyu da rabi da haihuwa kuma ta kwashe kimanin shekara daya ba ta sha magani ba.
An dai gwada ta kuma babu alamar cutar ko kadan a jikinta.
Masanan dai sun ce za su ci gaba da gwadata domin su tabbatar cewa irin maganin da aka yi mata zai iya yiwa sauran yara aiki.
Masu nazarin suna ganin sun samu nasara ne saboda sun tukarin cutar da wurin tun kafin ta samu inda za ta boye.
Dr Deborah Persaud ta ce idan har cutar ta samu makwanci ne a cikin jiki ta ke ginuwa har ta zuwa cutar AIDS.
Amma suna ganin wannan nasara da suka yi a kan yarinyar zai taimaka wajen samar da magani ga yara masu dauke da kwayar cutar ta HIV.
Idan har an tabbatar da lafiyar yarinyar, za ta zama mutun na biyu a duniya da aka samu cewa sun warke daga kwayar cutar.
Timothy Ray Brown ne ya zama mutun na farko da aka warkar da ga cutar ta HIV a shekara ta 2007.

Ana zaben kasar Kenya

 

Al'ummar kasar Kenya na babban zabe, abin da masana ke kallo a matsayin zabe mafi mahimmanci a tarihin kasar.
Wannan ne karo na farko da ake zabe a kasar, tun bayan da aka yi garanbawul ga kundin tsarin mulkin kasar domin kaucewa irin tashin hankalin da ya auku a kasar bayan zaben da aka gudanar a shekarar ta 2007.
Sama da mutane 1,000 ne da ba basa ga maciji da juna suka rasa rayukansu, bayan rikicin da ya barke a wancan lokacin.
Duk da cewa dai an yi ganganmi neman zaman lafiya, rahotanni sun ce an kashe jami'an 'yan sanda biyu a kusa da Mombasa da safiyar ranar Litinin.
Jami'ai sun ce wasu gungun mutane ne suka kaiwa 'yan sandan hari, a yankin Changamwe a bayan garin Mombasa.
Al'ummar Kenya za su zabi, 'yan majalisa da gwamnonin lardi da kuma yan majalisun lardi.
Sai dai duniya ta sanyan ido ne a kan zaben shugaban kasa.
'Yan takara takwas ne ke neman kujerar shugaban kasa, amma yan takarar dake gaba-gaba sune fira minista mai ci a yanzu, Raila Odinga da kuma Uhuru Kenyatta.

Sunday, 3 March 2013

Shugabannin jam'iyyar islama a Bangladesh sun yi kira a yi yajin aiki

Zanga-zanga a kasar Bangladesh

Shugabannin jam'iyyar islama a Bangladesh, sun yi kira a yi yajin aikin gama gari don nuna adawa da hukuncin kisan da aka yankewa daya daga cikin manyan jami'ansu.
An dai zarge su da aikata ta'asa lokacin yakin kwatar 'yanci daga Pakistan a shekarar 1971.

Hukumomi sun jibge karin jami'an tsaro gabanin fara yajin aikin.
Akalla mutane biyar ne suka rasa rayukansu a wata kwabzawa tsakanin jami'an tsaro da kuma magoya bayan jam'iyyar jama'atu islami tun a ranar alhamis.
Jagoran jam'iyyar 'yan kishin kasa ta Bangladesh Begum Khaleda Zia, ya dora alhakin tashin tashinar akan gwamnati.
Mr Khaleda ya ce dole ne gwamnati ta dakatar da kisan jama'a.Ina gargadin gwamnatin ta daina ko kuma abinda zai biyo baya ba zai kyau ba.

Sojoji a Afganistan sun nemi gafara kan kisan wasu yara

Dakarun kasar Australia

Dakarun kasa da kasa a Afganistan ISAF, sun nemi gafara game da kisan wasu yara makiyaya 'yan kasa da shekaru bakwai a lardin Uruzgan.
Yaran sun hallaka ne bayan da wani jirgi mai saukar angulu na dakarun kungiyar tsaro ta NATO ya bude musu wuta.

Wata sanarwa daga dakarun sojin ta ce sun aikata kisan ne bisa kuskure, bayan da suka zaci cewa 'yan kungiyar Taliban masu tada kayar baya ne, kuma sun ce za a biya iyalansu diyya.
Gwamnan lardin Uruzgan ya ce sojojin Australiar sun hallala yaran ne a bisa kuskure.
Jami'an kungiyar tsaro da NATO da na kasar Australia sun bayyana wannan kisa da cewa abin takaici ne.
A wata sanarwa, mai magana da yawun dakarun kasa da kasa na Afganistan, Janar Gunter Katz ya nemi gafara game da kisan.
A watan da ya gabata ne hare-haren dakarun kungiyar tsaro ta NATO ya hallaka fararen hula goma a lardin Kunar, da ya sa shugaban Afganistan Hamid Kharzai ya dakatar dakarun kasa da kasa kai hari da sama a yankunan gidajen jama'a.

Chadi ta ce sojojinta sun kashe wani jagoran 'yan tawaye a Mali

Sojojin kasar Chadi

Kasar Chadi ta ce sojojinta sun kashe daya daga cikin kusoshin 'yan kungiyar mayaka masu kaifin kishin Islama a yankin arewacin Afirka.
Ana dai zargin Jagoran kungiyar mai suna Mokhtar Belmokhtar da aka fi sani da '' Ido daya'' , da bayar da umarnin kai wani hari a masana'antar Iskar gas ta kasar Algeria a cikin watan Janairu.

Mutane fiye da talatin din da aka yi garkuwa da su ne suka hallaka harin.
Sojojin na kasar Chadi dake cikin tawagar dakarun kasashen Afirka ta yammar da aka tura kasar Mali, domin fatattakar 'yan tawaye masu kishin Islamar sun ce sun kashe Mokhtar Belmokhtar a wani hari da suka kai sansanin 'yan tawayen.
Mukaddashin hafsan sojin kasar ta Chadi, Janar Zakaria Ngonbongue ne ya sanar da batun kisan na Belmoktar, inda ya ce sun yi kaca kaca da babban sansanin 'yan tawayen.
Bayanan daga sojojin na kasar Chadin na zuwa ne kwana guda bayan da suka yi ikirarin cewa sun hallaka kwamanda kungiyar Al-Qaeda, Abu Zeid.
Sai dai babu wata majiya mai zaman kanta da ta tabbatar da mutuwar dukkannnin mutanen biyu.
Idan dai ta tabbata cewa an kashe Mokhtar Belmoktar, zai zama wani babban rashi nega kungiyar mayaka 'yan tawayen dake yankin arewacin Malin.
Sai dai ba wai zai nuna cewa an kawo kasrhen yakin ba, wanda 'yan tawayen ke ci gaba da nuna turjiya.
Belmokhat dai yayi ikirarin cewa shi ya jagoranci kai hari kan masana'antar sarrafa Iskar gas dake gabashin kasar Algeria a farkon wannan shekarar, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane sama da talatin, ciki har da wasu ma'aikata 'yan kasshen waje.

Saturday, 2 March 2013

Ba mu tsagaita bude wuta ba - BOKO HARAM

 Abubakar Shekau

Kungiyar Jama'atu Ahlil Sunnah Lid da'awati Wal Jihad da aka fi sani da Boko Haram, ta ce ba za ta yi sulhu da gwamnatin Najeriya ba, a cewar shugaban kungiyar Abubakar Shekau.
A wani sakon bidiyo na tsawon minti tara da aka rabawa manema labarai, Imam Abubakar Shekau ya musanta rahotannin da ake bayarwa na cewa ta dakatar da bude wuta kuma sun yi sulhu tare da hukumomin Najeriya.

Ba mu taba yin sulhu ba, kuma babu yadda za mu yi sulhu da gwamnati a halin da ake ciki," a cewar Shekau.
A baya an ruwaito wani mai suna Imam Abdulazeez a wani taron manema labarai a birnin Maiduguri na jihar Borno, yana cewa yana wakiltar shugaban kungiyar Imam Shekau ne, inda ya ayyana sulhu tsakanin kungiyar ta Boko Haram da gwamnati tare da dakatar da kai hare-hare.

'Ba abu ne mai yiwuwa ba'

Wannan dai shi ne sako na farko da shugaban na kungiyar Boko Haram ya fitar cikin lokaci mai tsawon gaske.
Shugaban na Boko Haram yace kwata-kwata bai san wani mutum mai suna Abdulazeez ba, wanda yayi ikirarin magana da yawun kungiyar, bare ma a yi batun cewa ya wakilce shi a taron manema labarai.
Abubakar Shekau ya nanata cewa batun sulhu da gwamnati a yanzu ba abu ne mai yiwuwa ba, saboda abin da ya kira kama 'yan-kungiyarsu ba dare ba rana da hukumomin Najeriya ke yi.
"Akwai ka'idojin sulhu da addinin Islama ya shimfida kuma wadannan ka'idodjin ne muke bi, amma yadda ake kama 'yan uwa ciki har da mata da kananan yara, alama ce ta cewa hukumomin Najeriya ba da gaske suke yi ba game da sulhu".
Jawabin na Abubakar Shekau dai bai kunshi batun wasu iyalan kasar Faransa su bakwai ba da aka sace a kasar Kamaru wadanda wani mutum da yayi ikirarin cewa shi dan kungiyar ne, ya ce su suka sace su ba.

Anyi tashin hankali a Conakry

 

Ma'aikatan kiwon lafiya a Guinea sun ce, an kashe mutum guda, wasu da dama kuma sun jikkata yayin da jami'an tsaro suka budewa wasu mutane wuta a yankin Koloma na Conakry, babban birnin kasar.
Wannan lamari dai ya biyo bayan kwanaki ne da aka kwashe ana tashin hankali a birnin tsakanin masu goyon bayan bangaren adawa da kuma jami'an tsaro, da kuma wadanda basa ga maciji da juna daga kabilu daban-daban.
Su dai 'yan adawar kasar suna nuna rashin nuna rashin amincewa ne da zaben da ake shirin yi cikin watan Mayu, suna zargin cewa, gwamnati ta shirya murde zaben.

Kenya: an kammala yaƙin neman zaɓe

 'Yan takara a Kenya

A ranar Asabar ne 'yan takarar shugabancin kasar Kenya suka yi gangamin yakin neman zabe na karshe, gabanin zaben kasa baki daya da za'a yi a Kenya ranar Litinin mai zuwa.
Na gaba gaba a takarar shugabancin kasar wato, Raila Odinga da Uhuru Kenyatta sun yi jawabai ga magoya bayansu a birnin Nairobi, inda suka yi kiran a zauna lafiya da juna
'Yan takara biyu dake kan gaba, wato Raila Odinga da Uhuru Kenyatta 'ya 'ya ne ga abokan gabar siyasa da su ka yi zamaninsu kusan shekaru hamsin da su ka gabata.
Tashin hankali dai ya biyo bayan zaben shugaban kasar Kenyan da aka yi shekaru biyar da su ka gabata, inda aka kashe mutane fiye da dubu.

Bafana na harin gasar cin kofin duniya

 Gordon Igesund

Kociyan Afrika ta Kudu Gordon Igesund ya ce ba zu su yi sakaci ba a lokacin da tawagarsa za ta koma fagen daga a wasan share fagen shiga gasar cin kofin duniya ta 2014.
Bafana Bafana za su kara da Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya a birnin Cape Town a ranar 23 ga watan Maris.
Kuma suna sane da cewa lallai suna bukatar nasara saboda sune na uku a rukunin A bayan da suka yi kunnen doki da Ethiopia da Botswana bara.
Kociya Igesund ya ce za a samu sauye-sauye a tawagar kasar wacce ta kai wasan dab da na kusa da na karshe a watan da ya gabata a gasar cin kofin kasashen Afrika wanda suka dauki bakunci.
"Ba ma cikin yanayin da ya dace a rukunin," a cewarsa. Mun zubar da maki hudu kuma wasanni hudu ne suka rage mana, a don haka an fara tsere mana.
Ethiopia ce ta daya a rukunin, sai Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya, sannan Afrika ta Kudu sai kuma Bostwana a matakin karshe.

Giggs zai ci gaba da zama a United

 Ryan Giggs

Ryan Giggs ya sake sanya hannu kan kwantiragin shekara daya da Manchester United.
Dan wasan mai shekaru 39, zai ci gaba da zama a United har zuwa watan Juni na shekara ta 2014.

Wannan na nufin zai shafe shekara ta 23 tare da babbar kungiyar kulob din.
Tsohon kyaftin din na Wales Giggs ya fara taka leda a United a ranar 2 ga watan Maris na 1991 sannan ya zira kwallaye 168 a wasanni 931.
"Ina jin dadin zama da kwallon da nake bugawa fiye da kowanne lokaci, mafi muhimmanci shi ne ina jin dadin gudummawar da nake bayarwa ga kulob din," a cewar Giggs.
"Wannan babban kulob ne da ya kamata mutum yaji dadin kasancewa tare da shi, kuma gashi muna sake kokarin daukar kofuna a daidai lokacin da kakar ke karewa."

Amurka za ta rage kashe kudade

Shugaban Amurka Barack Obama

Shugaban Amurka Barack Obama ya rattaba hannu kan dokar aiwatar da batun zaftare yawan kudaden da gwamnati ke kashewa.
Kudaden dai sun tasamma dala biliyan tamanin da biyar.

Dukkannin 'yayan jam'iyar Democrats da na Republicans sun nuna adawa da batun rage kudaden, sai dai bangarorin biyu sun gazan cimma yarjejeniya kan yadda zasu kawar da batun.
A shekaru biyun da suka gabata ne dai aka bullo da wannan yunkuri, aka kuma tsara shi ta yadda zai zaburar da 'yan siyasar Amurka wajen daidaita al'amuran da suka shafi harkokin kashe kudade.
Kusan rabin zaftare kudaden zai fito ne daga kasafin kudin bangaren harkokin tsaron kasar.
Shugaba Obama na gargadin cewa zaftare kudaden zai shafi yanayin samar da ayyuka dama habbakar tattalin arziki.

yakin neman zabe na karshe a Kenya

 Zabe a kasar Kenya

'Yan takara a zaben da za'a gudanar a kasar Kenya za su gudanar da gangamin yakin neman zabensu na karshe,kafin kada kuri'ar ranar Litinin.
Wannan zai kasance zaben farko da za a gudanar karkashin sabon kundin tsarin mulkin kasar da aka tsara domin kaucewa sake abkuwar mummunan rikicin kabilancin da aka tafka shekaru biyar da suka gabata.
Shugaban kasar Kenya Mwai Kibaki yayi kira ga 'yan kasar da su gudanar da zaben da za a yi ranar Litinin cikin kwanciyar hankali.
Mr Kibabki dai zai sauka daga mukaminsa bayan wa'adin mulki biyun da yayi.
A tattaunawarsa da BBC daya daga cikin na kan gaba gaba a fafatwar da za a yi a zaben shugaban kasar Firaminista Raila Odinga ya ce zai amince da duk wani sakamakon zaben idan bai samu galaba ba.
Biyu daga cikin 'yan takarar dake kan gaba gaba wato mudaddashen Firaminista, Uhuru Kenyatta da abokin takararsa, William Ruto dai na fuskantar tuhuma daga kotun hukunta aikata masu aikata laifukan yaki ta kasa da kasa, kan zaragin da ake musu da hannu a rikicin da ya faru a baya.
Mutane sama da dubu daya ne suka mutu a rikicn da ya faru a zaben shugaban kasar da aka gudanar a Kanyer cikin shekara ta 2007.

Friday, 1 March 2013

Goodluck Jonathan zai iya tsayawa takara a 2015'

Goodluck Jonathan

Wata kotun tarayya a Abuja babban birnin Najeriya ta ce shugaban kasar Goodluck Jonathan zai iya tsayawa takara a zaben shekara ta 2015.
Kotun ta ce sai a shekara ta 2015 ne zai kammala wa'adinsa na farko.

Goodluck Jonathan ya fara wa'adinsa ne bayan zaben da aka yi masa a shekara ta 2011.
Ta kara da cewa mulkin da ya hau a shekara ta 2010 bayan rasuwar marigayi Shugaba Umaru 'Yar'adua, ya zama wajibi ne domin cike gibin da aka samu kamar yadda tsarin mulki ya tanada.
Wani dan jam'iyyar PDP mai mulkin kasar ne ya shigar da karar yana neman kotu ta hana shugaban tsayawa takara bisa hasashen cewa ya yi wa'adi biyu a kan karagar mulki.
Wakiliyar BBC da ta halarci zaman kotun Raliya Zubairu, ta ce lauyoyin da suka wakilci jam'iyyar PDP sun nuna farin cikinsu ga wannan hukunci, sai dai wanda ya shigar da karar ya ce zai daukaka kara zuwa kotu ta gaba.

Mutane talatin sun hallaka a Bangladesh

 Rikici a kasar Bangladesh

Akalla mutane talatin ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu daruruwa kuma suka jikkata a zanga-zangar da ake a fadin kasar Bangladesh.
Zanga-zangar dai ta biyo bayan yankewa wani jagoran wata kungiyar musulmi hukuncin kisa, kan rawar da ya taka lokacin yakin neman 'yancin kasar daga Pakistan, shekaru sama da arba'in da suka wuce.
Wata kotu ce ta musamman ta samu Delwar Hussain Sayyadi na jam'iyyar jama'atu islami da laifin kisan kai da fyade da kuma azabtarwa.
A rikicin baya-bayan nan da akayi, an kashe jami'an 'yan sanda uku a gundumar arewacin Gaibanda lokacin da magoya bayan malamin su ke tarzoma.