Saturday, 9 March 2013

Uhuru Kenyata ya ce zai yi aiki tare da Raila Odinga

 Uhuru Kenyatta, zababben Shugaban Kenya

Sabon Zababban Shugaban Kasar Kenya Uhuru Kenyatta ya dau alkawarin aiki tare da wanda ya kayar, kuma abokin hamayyarsa Raila Odinga, da kuma yiwa dukkanin 'yan Kasar Kenya aiki a kalamansa ba kuma tare da tsoro ko nuna alfarma ba
An bayyana Mr Kenyatta wanda ya lashe zaben na ranar litinin da 'yar karamar , inda ya samu kashi hamsin da digo bakwai cikin dari na kuri'un da aka kada
Amma Mr Odingan yace zai kalubalanci sakamakon zaben a kotu.
Ya kuma yi gargadin cewar duk wani tashin hankali ka iya dagula kasar
Mr Kenyatta dai na fuskantar shari'ah a kotun hukunta manyan laifuka ta duniya dake Hague, bayan da aka zarge shi da hannu a tashin hankalin da ya biyo bayan zaben shekarar 2007

No comments:

Post a Comment