
Kociyan Afrika ta Kudu Gordon Igesund ya ce ba zu su
yi sakaci ba a lokacin da tawagarsa za ta koma fagen daga a wasan share
fagen shiga gasar cin kofin duniya ta 2014.
Bafana Bafana za su kara da Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya a birnin Cape Town a ranar 23 ga watan Maris.Kuma suna sane da cewa lallai suna bukatar nasara saboda sune na uku a rukunin A bayan da suka yi kunnen doki da Ethiopia da Botswana bara.
Kociya Igesund ya ce za a samu sauye-sauye a tawagar kasar wacce ta kai wasan dab da na kusa da na karshe a watan da ya gabata a gasar cin kofin kasashen Afrika wanda suka dauki bakunci.
"Ba ma cikin yanayin da ya dace a rukunin," a cewarsa. Mun zubar da maki hudu kuma wasanni hudu ne suka rage mana, a don haka an fara tsere mana.
Ethiopia ce ta daya a rukunin, sai Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya, sannan Afrika ta Kudu sai kuma Bostwana a matakin karshe.
No comments:
Post a Comment