
Gwamnatin jihar Kano ta ce ta cinma wasu shirye
shirye da wasu kamfanoni a Dubai, wadanda za su je Kanon su saka jari a
harkar da ta shafi sufurin jirgin kasa da zai rika zirga zirga a cikin
birnin Kano.
Baya ga wannan gwamnatin Kanon na tattaunawa da
wasu kamfanonin Dubai domin su zuba jari a bangaren hasken wutar
lantarki da kuma kafa jami'a mai zaman kanta.Gwamna Rabi'u Kwankwaso ya shaidawa cewa a watan gobe su ke sa ran daddalewa kan wadannan batutuwan da mutanen da suka gayyata zuwa Kano.
Jahar Kano dai ta yi fama da matsalolin hare haren 'yan bindiga abinda ya kawo cikas ga harkokin kasuwanci
No comments:
Post a Comment